< Luka 22 >

1 Anan nan idin gurasa mara yisti ya yi kusa, wanda a ke kira Idin ketarewa.
Estava perto a festa dos pães sem fermento, chamada de páscoa.
2 Manyan firistoci da marubuta suka yi shawara yadda za su kashe Yesu, gama suna jin tsoron mutane.
E os chefes dos sacerdotes, e os escribas procuravam um meio de o matar, pois eles temiam ao povo.
3 Shaidan ya shiga Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin goma sha biyun.
E Satanás entrou no Judas que era chamado Iscariotes, que era um dos doze.
4 Yahuza ya je ya yi shawara da manyan firistoci da Jarumawa yadda zai ba da Yesu a garesu.
E foi, e falou com os chefes dos sacerdotes e os oficiais, sobre como [o] entregaria para eles.
5 Suka yi farin ciki, suka yarda su ba shi kudi.
E [estes] se alegraram, e concordaram em lhe dar dinheiro.
6 Sai ya yarda, sai ya nimi dama yadda zai ba da shi garesu a lokacin da babu taro.
E [lhes] prometeu, e buscava oportunidade para o entregar quando não houvesse uma multidão.
7 Ranar idin gurasa mara yisti ya yi, da dole za a yi hadayan rago na Idin ketarewa.
E veio o dia dos [pães] sem fermento, em que se devia fazer o sacrifício da páscoa.
8 Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce masu, “Ku je ku shirya mana abincin Idin ketarewa, domin mu ci.”
E [Jesus] mandou a Pedro, e a João, dizendo: Ide, preparai-nos a páscoa, para que [a] comamos.
9 Suka tambaye shi, “A ina ka ke so mu shirya?”
E eles lhe disseram: Onde queres que [a] preparemos?
10 Ya amsa masu, “Ku ji, sa'adda ku ka shiga birnin, wani mutum mai dauke da tulun ruwa zai same ku. Ku bishi zuwa cikin gidan da za ya shiga.
E ele lhes disse: Eis que, quando entrardes na cidade, um homem com um vaso de água vos encontrará; segui-o até a casa onde ele entrar.
11 Sai ku gaya wa mai gidan, 'Malam ya ce, “Ina dakin baki, inda zan ci abincin Idin ketarewa da almajirai na?'”
E direis ao dono da casa: O Mestre te diz: Onde está o salão onde comerei a páscoa com meus discípulos?
12 Zai nuna maku babban bene wanda yake a shirye. Ku shirya a can.”
Então ele vos mostrará um grande salão já arrumado; preparai-a ali.
13 Sai suka tafi, suka sami komai kamar yadda ya gaya masu. Sai suka shirya abincin Idin ketarewan.
E indo eles, acharam como lhes tinha dito; e prepararam a páscoa.
14 Sa'adda lokacin ya yi, ya zauna da almajiran.
E vinda a hora, sentou-se [à mesa], e com ele os doze apóstolos.
15 Sai ya ce masu, “Ina da marmari matuka in ci wannan abincin Idin ketarewa da ku kamin in sha wahala.
E disse-lhes: Muito desejei comer convosco esta páscoa, antes que eu sofra.
16 Gama na ce maku, ba zan ci shi kuma ba, sai dai an cika shi a mulkin Allah.”
Porque eu vos digo, que dela não mais comerei, até que [isto] se cumpra no Reino de Deus.
17 Sai Yesu ya dauki koko, sa'adda ya yi godiya, sai yace, “Karba wannan, ku rarraba a tsakaninku.
E tomando o copo, e tendo agradecido [a Deus], disse: Tomai-o, e reparti [-o] entre vós.
18 Gama ina ce maku, ba zan sha wannan ruwan inabi kuma ba, sai dai mulkin Allah ya zo.”
Porque vos digo, que do fruto da videira eu não beberei, até que o Reino de Deus venha.
19 Sai ya dauki gurasa, sa'adda ya yi godiya, ya kakkarya shi, sai ya ba su, cewa, “Wannan jikina ne wanda aka bayar dominku. Ku yi wannan domin tunawa da ni.”
E tomando o pão, e tendo agradecido [a Deus], partiu-o, e o deu a eles, dizendo: Isto é o meu corpo, que é dado por vós; fazei isto em memória de mim.
20 Sai ya dauki kokon kuma bayan jibi, cewa, “Wannan koko sabon alkawari ne cikin jinina, wanda aka zubar dominku.
De modo semelhante também com o copo, depois da ceia, disse: Este copo [é] o Novo Testamento em meu sangue, que é derramado por vós.
21 Amma ku yi lura. Wanda zai bashe ni yana tare da ni a teburi.
Porém eis que a mão do que me trai [está] comigo à mesa.
22 Gama Dan Mutum zai tafi lallai kamar yadda aka kaddara. Amma kaiton wannan mutum da shine za ya bashe shi!”
E realmente o Filho do homem vai conforme o que está determinado; mas ai daquele homem por quem é traído!
23 Sai suka fara tambaya a tsakaninsu, wanene a cikinmu da zai yi wannan abu.
E começaram a perguntar entre si, qual deles seria o que faria isto.
24 Sai gardama ta tashi a tsakaninsu game da wanene mafi girma.
E houve também uma briga entre eles, sobre qual deles era considerado o maior.
25 Ya ce masu, “Sarakunan al'ummai suna nuna iko akansu, kuma wadanda suke da iko a kansu ana ce da su masu mulki da daraja.
E [Jesus] lhes disse: Os reis dos gentios os dominam, e os que exercem autoridade sobre eles são chamados de benfeitores;
26 Amma kada ya zama haka da ku. A maimakon haka, bari wanda ya ke mafi girma a cikinku ya zama mafi kankanta. Bari wanda yafi muhimmanci kuma ya zama kamar mai hidima.
Mas não [seja] assim entre vós; antes o maior de vós seja como o menor; e o que lidera, como o que serve.
27 Gama wanene yafi girma, wanda ya zauna a teburi, ko kuwa wanda yake yin hidima? Ba wanda ya zauna a teburi ba? Duk da haka ina kamar mai hidima a tsakaninku.
Porque qual é maior? O que se senta [à mesa], ou o que serve? Por acaso não é o que se senta [à mesa]? Porém eu estou entre vós como aquele que serve.
28 Amma ku ne wadanda ku ke tare da ni a cikin jarabobina.
E vós sois os que tendes permanecido comigo em minhas tentações.
29 Na baku mulki, kamar yadda Ubana ya ba ni mulki,
E eu vos determino um Reino, assim como meu pai o determinou a mim.
30 domin ku ci ku kuma sha a teburi na mulkina. Za ku zauna a kan kursiyai kuna shari'anta kabilun nan goma sha biyu na Israila.
Para que em meu Reino, comais e bebais à minha mesa; e vos senteis sobre tronos, julgando as doze tribos de Israel.
31 Siman, Siman, ka yi hankali, shaidan ya nemi izini a bada kai domin ya tankade ka kamar alkama.
Disse também o Senhor: Simão, Simão; eis que Satanás vos pediu, para [vos] peneirar como trigo;
32 Amma na yi maka addu'a, saboda kada bangaskiyarka ta fadi. Bayan da ka juyo kuma, ka karfafa 'yan'uwanka.”
Mas eu roguei por ti, que tua fé não se acabe; e quando tu te converteres, fortaleça teus irmãos.
33 Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina shirye in tafi tare da kai zuwa cikin kurkuku da zuwa mutuwa.”
E ele lhe disse: Senhor, estou preparado para ir contigo até à prisão, e à morte.
34 Yesu ya amsa masa, “Ina gaya maka, Bitrus, kamin caran zakara a yau, za ka yi musu na sau uku cewa ba ka sanni ba.”
Mas ele disse: Pedro, eu te digo que hoje o galo não cantará, antes que me negues três vezes que me conheces.
35 Sa'annan Yesu ya ce masu, “Lokacin da na aike ku babu jaka, ko burgami ko takalma, ko kun rasa wani abu? Sai suka amsa, “Babu.”
E disse a eles: Quando vos mandei sem bolsa, e sem sacola, e sem sandálias, por acaso algo vos faltou? E disseram: Nada.
36 Ya kuma ce masu, “Amma yanzu, wanda ya ke da jaka, bari ya dauka, da kuma burgami. Wanda ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa ya sayi guda.
Então, ele lhes disse: Mas agora, quem tem bolsa, tome-a, como também a sacola; e o que não tem espada, venda sua roupa, e compre uma.
37 Gama ina ce maku, abin da aka rubuta game da ni dole sai ya cika, 'An lisafta shi kamar daya daga cikin masu karya doka.' Gama abinda aka fada akaina ya cika.”
Porque eu vos digo, que ainda é necessário que se cumpra em mim aquilo que está escrito: E ele foi contado com os malfeitores. Porque aquilo que é sobre mim tem que se cumprir.
38 Sai suka ce, “Ubangiji, duba! Ga takuba biyu.” Sai ya ce masu, “Ya isa.”
E eles disseram: Senhor, eis aqui duas espadas. E ele lhes disse: É o suficiente.
39 Bayan cin abincin yamma, Yesu ya tafi, kamar yadda ya saba yi, zuwa dutsen Zaitun, sai almajiran suka bi shi.
E saindo, foi, como de costume, para o monte das Oliveiras; e os seus discípulos também o seguiram.
40 Sa'adda suka iso, ya ce masu, “Ku yi addu'a domin kada ku shiga cikin jaraba.”
E quando chegou a aquele lugar, disse-lhes: Orai para que não entreis em tentação.
41 Ya rabu da su misalin nisan jifa, sai ya durkusa kasa ya yi addu'a,
E se afastou deles, [à distância] de um tiro de pedra. E pondo-se de joelhos, orava,
42 yana cewa “Uba, in ka yarda, ka dauke wannan kokon daga gareni. Ko da yake ba nufina ba, amma bari naka nufin ya kasance.”
Dizendo: Pai, se tu quiseres, passa este copo de mim; porém não se faça minha vontade, mas a tua.
43 Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi.
E apareceu-lhe um anjo do céu, que o fortalecia.
44 Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.
E estando em angústia, orava mais intensamente. E seu suor se fez como gotas de sangue, que desciam até o chão.
45 Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu,
E ele, levantando-se da oração, veio a seus discípulos, e os achou dormindo por causa da tristeza.
46 sai ya tambaye su, “Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba.”
E disse-lhes: Por que estais dormindo? Levantai-vos, e orai, para que não entreis em tentação.
47 Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba,
E enquanto ele ainda estava falando, eis que uma multidão [chegou]; e um dos doze, o que se chamava Judas, ia adiante deles, e se aproximou de Jesus, para o beijar.
48 amma Yesu ya ce masa, “Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?”
E Jesus lhe disse: Judas, com um beijo trais ao Filho do homem?
49 Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?”
E os que estavam com ele, vendo o que iria acontecer, disseram-lhe: Senhor, feriremos com a espada?
50 Sai daya daga cikinsu ya kai wa bawan babban firist sara a kunne, sai ya yanke masa kunnensa na dama.
E um deles feriu a um servo do chefe dos sacerdotes, e cortou-lhe a orelha direita.
51 Yesu ya ce, “Ya isa haka.” Sai ya taba kunnensa, sai ya warkar da shi.
E respondendo Jesus, disse: Para com isto! E tocando-lhe a orelha, o curou.
52 Yesu yace wa manyan firistoci, da masu tsaron haikali, da dattawa wadanda suke gaba da shi, “Kun fito kamar za ku kama dan fashi, da takuba da sanduna?
E disse Jesus aos chefes dos sacerdotes, e aos oficiais do Templo, e aos anciãos, que tinham vindo contra ele: Como [se eu fosse] ladrão, saístes com espadas e bastões?
53 Sa'adda nake tare da ku kowace rana a haikali, ba ku kama ni ba. Amma wannan shine lokacinku, da kuma ikon duhu.”
Estando eu convosco todo dia no Templo, contra mim não me prendestes; mas esta é a vossa hora, e [sob] a autoridade das trevas.
54 Suka kama shi, sai suka tafi da shi, suka kawo shi cikin gidan babban firist. Amma Bitrus yana binsa daga nesa.
E prendendo-o, [o] trouxeram e o puseram na casa do sumo sacerdote. E Pedro [o] seguia de longe.
55 Bayan da suka hura wuta a tsakiyar gidan da suka zazzauna tare, Bitrus ya zaune a tsakaninsu.
E acenderam fogo no meio do pátio, e sentaram-se juntos, e Pedro se sentou entre eles.
56 Sai wata baranya ta ganshi ya zauna a hasken wuta, sai ta zura masa ido ta ce, “Wannan mutum ma yana tare da shi.”
E uma serva, vendo-o sentado junto ao fogo, fixando o olhos nele, disse: Este também estava com ele.
57 Amma Bitrus ya yi musu, yana cewa, “Mace, ban san shi ba.”
Porém ele o negou, dizendo: Mulher, eu não o conheço.
58 Bayan dan karamin lokaci sai wani mutum ya gan shi, sai ya ce, “Kaima kana daya daga cikinsu.” Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ba ni ba ne.”
E pouco depois, outro o viu, e disse: Também tu és um deles.
59 Bayan sa'a daya sai wani mutum ya nace da cewa, “Gaskiya wannan mutum yana tare da shi, gama shi dan Galili ne.”
E quando já tinha passado quase uma hora, outro afirmava, dizendo: Verdadeiramente também este estava com ele, porque também é galileu.
60 Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ban san abin da kake fada ba.” Sai nan da nan, da yana cikin magana, sai zakara ta yi cara.
E Pedro disse: Homem, não sei o que dizes. E logo, estando ele ainda falando, cantou o galo.
61 Yana juyawa, sai Ubangiji ya dubi Bitrus. Sai Bitrus ya tuna kalmar Ubangiji, sa'adda ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau za ka musunce ni sau uku.”
E o Senhor, virando-se, olhou para Pedro; e Pedro se lembrou da palavra do Senhor, como lhe tinha dito: Antes que o galo cante, tu me negarás três vezes.
62 Da fitowarsa waje, Bitrus ya yi kuka mai zafi.
E Pedro, saindo, chorou amargamente.
63 Sai mutanen da ke tsare da Yesu suka yi masa ba'a da bulala kuma.
E os homens que tinham prendido a Jesus zombavam dele, ferindo-o;
64 Bayan da suka rufe masa idanu, suka tambaye shi, cewa, “Ka yi annabci! Wa ya buge ka?”
E cobrindo-o, perguntavam, dizendo: Profetiza, quem é o que te feriu?
65 Suka yi wadansu miyagun maganganu na sabo game da Yesu.
E diziam muitas outras coisas contra ele, insultando-o.
66 Da gari ya waye, sai dattawa suka hadu tare, da manyan firistoci da marubuta. Sai suka kai shi cikin majalisa
E quando já era de dia, juntaram-se os anciãos do povo, e os chefes dos sacerdotes, e os escribas, e o trouxeram ao supremo conselho,
67 suka ce, “Gaya mana, in kai ne Almasihu.” Amma yace masu, “Idan na gaya maku, ba za ku gaskanta ba,
dizendo, Tu és o Cristo? Dize-nos. E ele lhes disse: Se eu vos disser, não o crereis.
68 idan na yi maku tambaya, ba za ku amsa ba.
E também se eu perguntar, não me respondereis, nem [me] soltareis.
69 Amma nan gaba, Dan Mutum zai zauna a hannun dama na ikon Allah.”
A partir de agora o Filho do homem se sentará à direita do poder de Deus.
70 Suka ce masa, “Ashe kai Dan Allah ne?” Sai Yesu ya ce masu, “Haka kuka ce, nine.”
E todos disseram: Então tu és o Filho de Deus? E ele lhes disse: Vós dizeis que eu sou.
71 Suka ce, “Don me muke neman shaida? Gama mu da kanmu munji daga bakinsa.”
E eles disseram: Para que precisamos de mais testemunho? Pois nós mesmos o ouvimos de sua boca.

< Luka 22 >