< Luka 1 >

1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Ker so že mnogi vzeli v roko, da po vrsti uredijo izjavo o teh stvareh, ki se najbolj gotovo verjamejo med nami,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
celo kakor so nam jih izročili [tisti], ki so bili od začetka priče in služabniki besede,
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
se je tudi meni zdelo dobro, od samega začetka imeti popolno razumevanje o vseh stvareh, da tebi, nadvse odlični Teófil, napišem po vrsti,
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
da lahko spoznaš zanesljivost o teh besedah, o katerih si bil poučen.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
V dneh Heroda, judejskega kralja, je bil nek duhovnik, imenovan Zaharija, iz Abíjeve skupine, in njegova žena je bila izmed Aronovih hčera in njeno ime je bilo Elizabeta.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
Oba sta bila pravična pred Bogom in sta brez krivde živela po vseh Gospodovih zapovedih in odredbah.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
Ker je bila Elizabeta jalova nista imela nobenega otroka in oba sta bila zelo zvrhana v letih.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
In pripetilo se je, medtem ko je pred Bogom opravljal duhovniško službo, po vrstnem redu svoje skupine,
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
glede na navado duhovniške službe, je bil na njem žreb, da zažge kadilo, ko je odšel v Gospodov tempelj.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
Celotna množica ljudi pa je ob času zažiganja kadila zunaj molila.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
In prikazal se mu je Gospodov angel, stoječ na desni strani kadilnega oltarja.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
Ko pa ga je Zaharija zagledal, se je vznemiril in strah ga je spreletel.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
Toda angel mu je rekel: »Ne boj se, Zaharija, kajti tvoja molitev je uslišana in tvoja žena Elizabeta ti bo rodila sina in ti boš klical njegovo ime Janez.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
Imel boš radost in veselje in mnogi se bodo veselili ob njegovem rojstvu.
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
Kajti velik bo v Gospodovih očeh in ne bo pil niti vina niti močne pijače in celó od maternice svoje matere bo izpolnjen s Svetim Duhom.
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
In mnoge izmed Izraelovih otrok bo obrnil h Gospodu, njihovemu Bogu.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
Pred njim bo šel z Elijevim duhom in močjo, da obrne srca očetov k otrokom in neposlušne k modrosti pravičnih; da pripravi ljudstvo, pripravljeno za Gospoda.«
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
Zaharija je angelu rekel: »Po čem bom to spoznal? Kajti starec sem in moja žena je zelo zvrhana v letih.«
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
Angel mu odgovori in reče: »Jaz sem Gabriel, ki stojim v prisotnosti Boga in poslan sem, da ti govorim in da ti pokažem te vesele novice.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
Glej, ker nisi verjel mojim besedam, ki se bodo uresničile ob njihovem pravem času, boš postal nem in ne boš mogel govoriti do dne, ko se bodo te besede izpolnile.«
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
In ljudje so čakali na Zaharija in se čudili, da se je tako dolgo mudil v templju.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
Ko pa je prišel ven, jim ni mogel spregovoriti, in zaznali so, da je videl v templju videnje, kajti dajal jim je znamenja, ostal pa je brez besed.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
Pripetilo se je, kakor hitro so bili dnevi njegovega služenja dovršeni, da se je odpravil k svoji lastni hiši.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
Po teh dneh je njegova žena Elizabeta spočela in se pet mesecev skrivala, rekoč:
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
»Tako je Gospod ravnal z menoj v dneh, v katerih je pogledal name, da odvzame mojo grajo izmed ljudi.«
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
V šestem mesecu pa je bil od Boga poslan angel Gabriel v galilejsko mesto, imenovano Nazaret,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
k devici, zaročeni z možem, katerega ime je bilo Jožef, iz Davidove hiše; in devici je bilo ime Marija.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
Angel je vstopil k njej in rekel: »Pozdravljena, ti, ki si zelo spoštovana, Gospod je s teboj, blagoslovljena si med ženskami.«
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
Ko pa ga je zagledala, je bila ob njegovem govoru zaskrbljena in v svojih mislih preudarjala, kakšne vrste pozdrav naj bi to bil.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
Angel ji je rekel: »Ne boj se, Marija, kajti pri Bogu si našla naklonjenost.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
Glej, v svoji maternici boš spočela in rodila sina in njegovo ime boš klicala JEZUS.
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
Velik bo in imenovan bo Sin Najvišjega; in Gospod Bog mu bo dal prestol njegovega očeta Davida
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
in nad Jakobovo hišo bo vladal večno in njegovemu kraljestvu ne bo konca.« (aiōn g165)
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
Potem je Marija rekla angelu: »Kako se bo to zgodilo, glede na to, da ne poznam moškega?«
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
Angel je odgovoril in ji rekel: »Sveti Duh bo prišel nadte in moč Najvišjega te bo obsenčila, zato bo tudi ta sveta oseba, ki bo rojena od tebe, imenovana Božji Sin.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
Glej, tvoja sestrična Elizabeta je prav tako v svoji visoki starosti spočela sina, in to je šesti mesec z njo, ki je bila imenovana jalova.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
Kajti z Bogom nič ne bo nemogoče.«
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
Marija je rekla: »Glej, Gospodova pomočnica; naj se mi zgodi glede na tvojo besedo.« In angel je odšel od nje.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
Marija je v tistih dneh vstala in z naglico odšla v hribovito deželo, v Judovo mesto
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
in vstopila v Zaharijevo hišo ter pozdravila Elizabeto.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
In pripetilo se je, ko je Elizabeta zaslišala Marijin pozdrav, da je dete poskočilo v njeni maternici in Elizabeta je bila izpolnjena s Svetim Duhom
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
in zaklicala z močnim glasom ter rekla: »Blagoslovljena si ti med ženskami in blagoslovljen je sad tvoje maternice.
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
Od kod je meni to, da bi prišla k meni mati mojega Gospoda?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
Kajti glej, brž ko je glas tvojega pozdrava zazvenel v mojih ušesih, je dete v moji maternici od radosti poskočilo.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
Blagoslovljena je tista, ki je verovala, kajti izpolnile se bodo te besede, ki so ji bile povedane od Gospoda.«
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Marija je rekla: »Moja duša poveličuje Gospoda
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
in moj duh se veseli v Bogu, mojem Odrešeniku.
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
Kajti ozrl se je na nizek stan svoje pomočnice, kajti glej, odslej me bodo vsi rodovi imenovali blagoslovljeno.
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
Kajti tisti, ki je mogočen, mi je storil velike stvari in sveto je njegovo ime.
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
In njegovo usmiljenje je od roda do roda nad tistimi, ki se ga bojijo.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
S svojim laktom je pokazal moč, ponosne je razgnal v domišljiji njihovih src.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
Mogočne je odstranil z njihovih prestolov in povišal te z nizkim položajem.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
Lačne je napolnil z dobrinami, bogate pa je odpustil prazne.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
Pomagal je svojemu služabniku Izraelu, v spomin na svoje usmiljenje,
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
kakor je govoril našim očetom, Abrahamu in njegovemu semenu na veke.« (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
Marija je z njo ostala približno tri mesece in se vrnila v svojo lastno hišo.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Torej prišel je Elizabetin polni čas, ko naj bi rodila; in rodila je sina.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
Njeni sosedje in njeni sorodniki so slišali, kako je Gospod nad njo izkazal veliko usmiljenje in veselili so se z njo.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
Pripetilo pa se je, da so na osmi dan prišli, da obrežejo otroka in poimenovali so ga Zaharija, po imenu njegovega očeta.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
Njegova mati pa je odgovorila in rekla: »Ne tako, temveč se bo imenoval Janez.«
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
Oni pa so ji rekli: »Nikogar v tvojem sorodstvu ni, ki je poimenovan s tem imenom.«
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
In naredili so znamenja njegovemu očetu, kako bi ga on imenoval.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
In prosil je za pisalno deščico ter napisal, rekoč: »Njegovo ime je Janez.« In vsi so se čudili.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
In njegova usta so se takoj odprla in njegov jezik se je sprostil in spregovoril je ter hvalil Boga.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
In strah je prišel na vse, ki so prebivali naokoli njih; in vse te besede so se razglasile naokoli po vsej judejski hriboviti deželi.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
In vsi, ki so jih slišali, so si jih položili v svoja srca, rekoč: »Kakšne vrste otrok bo to!« In Gospodova roka je bila z njim.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
In njegov oče Zaharija je bil izpolnjen s Svetim Duhom in prerokoval, rekoč:
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
»Blagoslovljen bodi Gospod, Izraelov Bog; kajti obiskal je in odkupil svoje ljudi
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
in za nas je dvignil rog rešitve duš v hiši svojega služabnika Davida,
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
kakor je govoril po ustih svojih svetih prerokov, ki so bili, odkar je svet nastal, (aiōn g165)
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
da bi bili mi lahko rešeni pred našimi sovražniki in iz roke vseh, ki nas sovražijo,
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
da opravi usmiljenje, obljubljeno našim očetom in se spomni svoje svete zaveze,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
prisege, s katero je prisegel našemu očetu Abrahamu,
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
da nam bo zagotovil, da mu bomo osvobojeni iz roke svojih sovražnikov, lahko služili brez strahu,
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
v svetosti in pravičnosti pred njim, vse dni našega življenja.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
Ti pa, otrok, boš imenovan prerok Najvišjega, kajti šel boš pred Gospodov obraz, da pripraviš njegove poti,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
da daš njegovim ljudem spoznanje o rešitvi duš z odpuščanjem njihovih grehov,
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
po nežnem usmiljenju našega Boga; po katerem nas je obiskalo svitanje od zgoraj,
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
da da svetlobo tem, ki sedijo v temi in v smrtni senci, da vodi naša stopala na pot miru.«
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
Otrok pa je rasel in se krepil v duhu in bil je v puščavah do dneva njegove pojavitve Izraelu.

< Luka 1 >