< Luka 1 >

1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Forasmuch as many haue taken in hand to set foorth the storie of those things, whereof we are fully persuaded,
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
As they haue deliuered them vnto vs, which from the beginning saw them their selues, and were ministers of ye word,
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
It seemed good also to me (most noble Theophilus) assoone as I had searched out perfectly all things from the beginning, to write vnto thee thereof from point to point,
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
That thou mightest acknowledge the certaintie of those things, whereof thou hast bene instructed.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
In the time of Herod King of Iudea, there was a certaine Priest named Zacharias, of the course of Abia: and his wife was of the daughters of Aaron, and her name was Elisabet.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
Both were iust before God, and walked in all the commandements and ordinances of the Lord, without reproofe.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
And they had no childe, because that Elisabet was barren: and both were well stricken in age.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
And it came to passe, as he executed the Priestes office before God, as his course came in order,
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
According to the custome of the Priests office, his lot was to burne incense, when he went into the Temple of the Lord.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
And the whole multitude of the people were without in prayer, while the incense was burning.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
Then appeared vnto him an Angel of the Lord standing at the right side of the altar of incense.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
And when Zacharias sawe him, he was troubled, and feare fell vpon him.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
But the Angel saide vnto him, Feare not, Zacharias: for thy prayer is heard, and thy wise Elisabet shall beare thee a sonne, and thou shalt call his name Iohn.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
And thou shalt haue ioy and gladnes, and many shall reioyce at his birth.
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
For he shalbe great in the sight of the Lord, and shall neither drinke wine, nor strong drinke: and he shalbe filled with the holy Ghost, euen from his mothers wombe.
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
And many of the children of Israel shall he turne to their Lord God.
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
For he shall goe before him in the spirite and power of Elias, to turne the hearts of the fathers to the children, and the disobedient to the wisedome of the iust men, to make ready a people prepared for the Lord.
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
Then Zacharias said vnto ye Angel, Whereby shall I knowe this? for I am an olde man, and my wife is of a great age.
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
And the Angell answered, and sayde vnto him, I am Gabriel that stand in the presence of God, and am sent to speake vnto thee, and to shew thee these good tidings.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
And beholde, thou shalt be domme, and not be able to speake, vntill the day that these things be done, because thou beleeuedst not my words, which shalbe fulfilled in their season.
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Now the people waited for Zacharias, and marueiled that he taried so long in the Temple.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
And when hee came out, hee coulde not speake vnto them: then they perceiued that hee had seene a vision in the Temple: For he made signes vnto them, and remained domme.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
And it came to passe, when the daies of his office were fulfilled, that he departed to his owne house.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
And after those daies, his wife Elisabet conceiued, and hid her selfe fiue moneths, saying,
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
Thus hath the Lord dealt with me, in the daies wherein he looked on me, to take from me my rebuke among men.
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
And in the sixth moneth, the Angell Gabriel was sent from God vnto a citie of Galile, named Nazareth,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
To a virgin affianced to a man whose name was Ioseph, of the house of Dauid, and the virgins name was Marie.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
And the Angel went in vnto her, and said, Haile thou that art freely beloued: the Lord is with thee: blessed art thou among women.
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
And when she saw him, she was troubled at his saying, and thought what maner of salutation that should be.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
Then the Angel saide vnto her, Feare not, Marie: for thou hast found fauour with God.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
For loe, thou shalt conceiue in thy wobe, and beare a sonne, and shalt call his name Iesus.
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
He shall be great, and shall be called the Sonne of the most High, and the Lord God shall giue vnto him the throne of his father Dauid.
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
And hee shall reigne ouer the house of Iacob for euer, and of his kingdome shall bee none ende. (aiōn g165)
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
Then sayde Marie vnto the Angel, How shall this be, seeing I knowe not man?
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
And the Angel answered, and said vnto her, The holy Ghost shall come vpon thee, and the power of the most High shall ouershadowe thee: therefore also that holy thing which shall bee borne of thee, shall be called the Sonne of God.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
And behold, thy cousin Elisabet, she hath also conceiued a sonne in her olde age: and this is her sixt moneth, which was called barren.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
For with God shall nothing be vnpossible.
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
Then Marie said, Behold the seruant of the Lord: be it vnto me according to thy woorde. So the Angel departed from her.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
And Marie arose in those daies, and went into ye hil countrey with hast to a citie of Iuda,
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
And entred into the house of Zacharias, and saluted Elisabet.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
And it came to passe, as Elisabet heard the salutation of Marie, the babe sprang in her bellie, and Elisabet was filled with the holy Ghost.
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
And she cried with a loud voice, and saide, Blessed art thou among women, because the fruit of thy wombe is blessed.
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
And whence commeth this to mee, that the mother of my Lord should come to me?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
For loe, assoone as the voice of thy salutation sounded in mine eares, the babe sprang in my bellie for ioye,
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
And blessed is shee that beleeued: for those things shall be perfourmed, which were tolde her from the Lord.
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Then Marie sayde, My soule magnifieth the Lord,
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
And my spirite reioyceth in God my Sauiour.
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
For hee hath looked on the poore degree of his seruaunt: for beholde, from henceforth shall all ages call me blessed,
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
Because hee that is mightie, hath done for me great things, and holy is his Name.
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
And his mercie is from generation to generation on them that feare him.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
Hee hath shewed strength with his arme: hee hath scattered the proude in the imagination of their hearts.
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
Hee hath put downe the mighty from their seates, and exalted them of lowe degree.
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
Hee hath filled the hungrie with good things, and sent away the rich emptie.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
Hee hath vpholden Israel his seruaunt to be mindefull of his mercie
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
(As hee hath spoken to our fathers, to wit, to Abraham, and his seede) for euer. (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
And Marie abode with her about three moneths: after, shee returned to her owne house.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Nowe Elisabets time was fulfilled, that shee should be deliuered, and shee brought foorth a sonne.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
And her neighbours, and cousins heard tell howe the Lord had shewed his great mercie vpon her, and they reioyced with her.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
And it was so that on the eight day they came to circumcise the babe, and called him Zacharias after the name of his father.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
But his mother answered, and saide, Not so, but he shalbe called Iohn.
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
And they saide vnto her, There is none of thy kindred, that is named with this name.
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
Then they made signes to his father, howe he would haue him called.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
So hee asked for writing tables, and wrote, saying, His name is Iohn, and they marueiled all.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
And his mouth was opened immediately, and his tongue, and he spake and praised God.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
Then feare came on all them that dwelt neere vnto them, and all these woordes were noised abroade throughout all the hill countrey of Iudea.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
And al they that heard them, laid them vp in their hearts, saying, What maner childe shall this be! and the hand of the Lord was with him.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
Then his father Zacharias was filled with the holy Ghost, and prophesied, saying,
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
Blessed be the Lord God of Israel, because he hath visited and redeemed his people,
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
And hath raised vp the horne of saluation vnto vs, in the house of his seruant Dauid,
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
As he spake by ye mouth of his holy Prophets, which were since the world began, saying, (aiōn g165)
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
That he would sende vs deliuerance from our enemies, and from the hands of all that hate vs,
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
That he might shewe mercie towards our fathers, and remember his holy couenant,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
And the othe which he sware to our father Abraham.
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
Which was, that he would graunt vnto vs, that we being deliuered out of the handes of our enemies, should serue him without feare,
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
All the daies of our life, in holinesse and righteousnesse before him.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
And thou, babe, shalt be called the Prophet of the most High: for thou shalt goe before the face of the Lord, to prepare his waies,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
And to giue knowledge of saluation vnto his people, by the remission of their sinnes,
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
Through ye tender mercy of our God, wherby the day spring from an hie hath visited vs,
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
To giue light to them that sit in darknes, and in the shadow of death, and to guide our feete into the way of peace.
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
And the childe grewe, and waxed strong in spirit, and was in the wildernesse, til the day came that he should shewe him selfe vnto Israel.

< Luka 1 >