< Yohanna 17 >

1 Da Yesu ya fadi wandannan abubuwa, sai ya tada idanunsa sama ya ce, ya Uba, sa'a ta zo; ka daukaka Danka, domin Dan shi ya daukaka ka,
These words spake Jesus, and lifted up his eyes to heaven, and said, Father, the hour is come; glorify thy Son, that thy Son also may glorify thee:
2 kamar yadda ka ba shi iko akan dukkan 'yan adam, ya ba da rai madawwami ga duk wanda ka ba shi. (aiōnios g166)
As thou hast given him power over all flesh, that he should give eternal life to as many as thou hast given him. (aiōnios g166)
3 Wannan ne rai madawwami: wato su san ka, Allah makadaici na gaskiya, da shi kuma wanda ka aiko, Yesu Almasihu. (aiōnios g166)
And this is life eternal, that they might know thee the only true God, and Jesus Christ, whom thou hast sent. (aiōnios g166)
4 Na daukaka ka a duniya, na gama aikin da ka ba ni in yi.
I have glorified thee on the earth: I have finished the work which thou gavest me to do.
5 Yanzu, ya Uba, ka daukaka ni tare da kai da daukaka wadda ni ke da ita tare da kai tun kafin duniya ta kasanci.
And now, O Father, glorify thou me with thine own self with the glory which I had with thee before the world was.
6 Na bayyana sunanka ga mutunen da ka ba ni acikin duniya. Na ka suke, ka ba ni su, sun kuwa kiyaye maganarka.
I have manifested thy name unto the men which thou gavest me out of the world: thine they were, and thou gavest them me; and they have kept thy word.
7 Yanzu kuwa sun san duk iyakar abinda ka ba ni daga gare ka yake,
Now they have known that all things whatsoever thou hast given me are of thee.
8 don kuwa maganganun da ka fada mani. Na fada masu, sun kuma karba, sun sani kuwa hakika na fito daga gareka ne, kuma sun gaskata kai ne ka aiko ni.
For I have given unto them the words which thou gavest me; and they have received [them], and have known surely that I came out from thee, and they have believed that thou didst send me.
9 Ina yi masu addu'a. Ba domin duniya ni ke yin addu'a ba, amma domin wadanda ka bani gama na ka ne.
I pray for them: I pray not for the world, but for them which thou hast given me; for they are thine.
10 Gama dukan abinda ke nawa na ka ne, naka kuwa nawa ne, an kuma daukaka ni a cikinsu.
And all mine are thine, and thine are mine; and I am glorified in them.
11 Ba na cikin duniya kuma, amma wadannan mutane suna cikin duniya, ni kuwa ina zuwa wurin ka. Ya Uba mai Tsarki, ka adanasu cikin sunanka da ka ba ni domin su zama daya, kamar dai yadda muke daya.
And now I am no more in the world, but these are in the world, and I come to thee. Holy Father, keep through thine own name those whom thou hast given me, that they may be one, as we [are].
12 Lokacin da ina tare da su, na adanasu acikin sunanka da ka ba ni. Na kiyaye su, kuma ko daya kuwa daga cikinsu ba ya bace ba, sai dai dan hallakar nan, domin Nassi ya cika.
While I was with them in the world, I kept them in thy name: those that thou gavest me I have kept, and none of them is lost, but the son of perdition; that the scripture might be fulfilled.
13 Amma yanzu ina zuwa wurinka, Ina fadar wadannan abubuwa tun ina duniya, domin farin cikina ya zama cikakke a zukatansu.
And now come I to thee; and these things I speak in the world, that they might have my joy fulfilled in themselves.
14 Na ba su maganarka, kuma duniya ta tsane su domin su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
I have given them thy word; and the world hath hated them, because they are not of the world, even as I am not of the world.
15 Ba ina roko ka dauke su daga cikin duniya ba, amma domin ka tsare su daga mugun nan.
I pray not that thou shouldest take them out of the world, but that thou shouldest keep them from the evil.
16 Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
They are not of the world, even as I am not of the world.
17 Ka kebe su domin kanka cikin gaskiya. maganarka gaskiya ce.
Sanctify them through thy truth: thy word is truth.
18 Kamar dai yadda ka aiko ni cikin duniya, haka kuma na aike su cikin duniya.
As thou hast sent me into the world, even so have I also sent them into the world.
19 Na kebe kaina gareka sabili da su, domin su ma kansu a kebe su gareka cikin gaskiya.
And for their sakes I sanctify myself, that they also might be sanctified through the truth.
20 Ina addu'a ba domin wadannan kadai ba, amma har da wadanda zasu gaskata da ni ta wurin maganarsu,
Neither pray I for these alone, but for them also which shall believe on me through their word;
21 Domin su zama daya dukansu, kamar yadda kai, ya Uba, ka ke ciki na, ni kuma na ke cikin ka. Ina roko suma su kasance a cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa ka aiko ni
That they all may be one; as thou, Father, [art] in me, and I in thee, that they also may be one in us: that the world may believe that thou hast sent me.
22 Daukakar da ka bani, ita nake basu, domin su zama daya, kamar yadda mu ke daya;
And the glory which thou gavest me I have given them; that they may be one, even as we are one:
23 ni a cikinsu, kai kuma a ciki na. Domin su kammalu cikin zama daya, domin duniya ta sani cewa ka aiko ni, kuma ka kaunace su, kamar yadda ka kaunace ni.
I in them, and thou in me, that they may be made perfect in one; and that the world may know that thou hast sent me, and hast loved them, as thou hast loved me.
24 Ya Uba, ina so wadanda ka ba ni, su ma su kasance tare da ni inda nake, domin su dubi daukakata da ka yi mani. Domin ka kaunace ni tun kafin halittar duniya.
Father, I will that they also, whom thou hast given me, be with me where I am; that they may behold my glory, which thou hast given me: for thou lovedst me before the foundation of the world.
25 Ya Uba mai adalci, duniya kam, ba ta sanka ba, amma ni na sanka; kuma wadannan sun sani kai ne ka aiko ni.
O righteous Father, the world hath not known thee: but I have known thee, and these have known that thou hast sent me.
26 Na sanar masu da sunanka, zan kuma sanar da shi domin kaunar da ka yi mani ta kasance a cikinsu, ni kuma in kasance a cikinsu,
And I have declared unto them thy name, and will declare [it]: that the love wherewith thou hast loved me may be in them, and I in them.

< Yohanna 17 >