< Ayyukan Manzanni 4 >

1 Yayin da Bitrus da Yahaya suna kan magana da mutanen, sai firistoci da shugaban masu tsaron Haikali da kuma Sadukiyawa suka afko masu.
And as they are speaking unto the people, there came to them the priests, and the magistrate of the temple, and the Sadducees —
2 Sun damu sosai domin Bitrus da Yahaya suna koyar da mutane game da Yesu kuma suna shelar tashinsa daga matattu.
being grieved because of their teaching the people, and preaching in Jesus the rising again out of the dead —
3 Suka kama su suka jefa kurkuku sai washegari, domin yamma ta riga ta yi.
and they laid hands upon them, and did put them in custody unto the morrow, for it was evening already;
4 Amma mutane da yawa da suka ji sakon suka ba da gaskiya; kimanin mazaje dubu biyar ne kuwa suka ba da gaskiya.
and many of those hearing the word did believe, and the number of the men became, as it were, five thousand.
5 Washegari, da shugabaninsu, da dattawansu, da Marubuta suka taru a Urushalima.
And it came to pass upon the morrow, there were gathered together of them the rulers, and elders, and scribes, to Jerusalem,
6 Anas babban firist, yana nan, da Kayafa, da Yahaya da Iskandari, da dukan dangin babban firist
and Annas the chief priest, and Caiaphas, and John, and Alexander, and as many as were of the kindred of the chief priest,
7 Da suka kawo Bitrus da Yahaya a tsakiyarsu sai suka tambaye su, “Da wanne iko, ko cikin wanne suna k ka yi haka?”
and having set them in the midst, they were inquiring, 'In what power, or in what name did ye do this?'
8 Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya ce, “Ku shugabanni da dattawan jama'a,
Then Peter, having been filled with the Holy Spirit, said unto them: 'Rulers of the people, and elders of Israel,
9 idan mu yau ana tuhumarmu saboda aikin kirki da aka yi ga wannan mara lafiya - ta yaya wannan mutum ya sami lafiya?
if we to-day are examined concerning the good deed to the ailing man, by whom he hath been saved,
10 Bari ku da dukan mutanen Isra'ila, ku san wannan, cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, wanda kuka giciye, wanda Allah ya tayar daga matattu ta dalilinsa ne wannan mutumin yake tsaye a gaban ku lafiyayye.
be it known to all of you, and to all the people of Israel, that in the name of Jesus Christ of Nazareth, whom ye did crucify, whom God did raise out of the dead, in him hath this one stood by before you whole.
11 Yesu Almasihu ne dutsen da ku magina kuka ki, amma an mai da shi kan gini.
'This is the stone that was set at nought by you — the builders, that became head of a corner;
12 Babu ceto daga kowanne mutum, domin babu wani suna da aka bayar karkashin sama, a cikin mutane wanda ta wurinsa za a iya samu ceto.''
and there is not salvation in any other, for there is no other name under the heaven that hath been given among men, in which it behoveth us to be saved.'
13 Sa'adda, suka ga karfin halin Bitrus da Yahaya, suka gane mutane ne talakawa marasa ilimi, sai suka yi mamaki, suka kuma lura suka gane Bitrus da Yahaya sun kasance tare da Yesu.
And beholding the openness of Peter and John, and having perceived that they are men unlettered and plebeian, they were wondering — they were taking knowledge also of them that with Jesus they had been —
14 Da yake suna ganin mutumin nan da aka warkar tare da su, sai suka rasa abin yi.
and seeing the man standing with them who hath been healed, they had nothing to say against [it],
15 Amma bayan sun fitar da manzannin daga majalisa sai suka tattauna a tsakaninsu.
and having commanded them to go away out of the sanhedrim, they took counsel with one another,
16 Suka ce, “Yaya za mu yi da wadannan mutane? Babu shakka aikin al'ajibi ya faru ta wurinsu, kuma sananne ne ga dukan mazauna Urushalima, kuma ba mu da iko mu musanci haka.
saying, 'What shall we do to these men? because that, indeed, a notable sign hath been done through them, to all those dwelling in Jerusalem [is] manifest, and we are not able to deny [it];
17 Amma saboda kada ya cigaba da yaduwa cikin mutane, bari mu yi masu kashedi kada su kara magana da kowa cikin wannan suna.''
but that it may spread no further toward the people, let us strictly threaten them no more to speak in this name to any man.'
18 Suka kira Bitrus da Yahaya suka dokace su kada su kara magana ko kuma koyarwa ko kadan a cikin sunan Yesu.
And having called them, they charged them not to speak at all, nor to teach, in the name of Jesus,
19 Amma Bitrus da Yahaya suka amsa suka ce, ''Ko ya yi daidai a gaban Allah mu yi maku biyayya fiye da shi, ku hukunta.
and Peter and John answering unto them said, 'Whether it is righteous before God to hearken to you rather than to God, judge ye;
20 Baza mu iya daina magana game da abubuwan da muka ji kuma muka gani ba.''
for we cannot but speak what we did see and hear.'
21 Bayan sun sake yi wa Bitrus da yahaya kashedi, sai suka sake su, su tafi. Domin ba su iya samu wata hujja da za su hore su a kai ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
And they having further threatened [them], let them go, finding nothing how they may punish them, because of the people, because all were glorifying God for that which hath been done,
22 Mutumin da ya sami wannan al'ajibi na warkarwa yana sama da shekara arba'in.
for above forty years of age was the man upon whom had been done this sign of the healing.
23 Bayan an sake su, Bitrus da Yahaya suka zo cikin mutanensu suka ba da rahoton duk abin da manyan firistoci da dattawa suka fada masu.
And being let go, they went unto their own friends, and declared whatever the chief priests and the elders said unto them,
24 Da suka ji haka, suka daga muryarsu tare ga Allah suka ce, ''Ubangiji, kai da ka yi sama da duniya da teku da duk abin da ke cikinsu,
and they having heard, with one accord did lift up the voice unto God, and said, 'Lord, thou [art] God, who didst make the heaven, and the earth, and the sea, and all that [are] in them,
25 kai wanda ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin ubanmu Dauda bawanka, ya ce, 'Me ya sa al'ummai suka tunzura, kuma mutane suke tunanin abubuwan banza?
who, through the mouth of David thy servant, did say, Why did nations rage, and peoples meditate vain things?
26 Sarakunan duniya sun hada kansu tare, kuma shugabanninsu sun taru don su yi gaba da Ubangiji, da kuma Almasihunsa.'
the kings of the earth stood up, and the rulers were gathered together against the Lord and against His Christ;
27 Hakika, Hiridus da Buntus Bilatus, tare da al'ummai da mutanen Isra'ila, sun taru a wannan birni domin su yi jayayya da bawanka mai tsarki Yesu, shafaffe.
for gathered together of a truth against Thy holy child Jesus, whom Thou didst anoint, were both Herod and Pontius Pilate, with nations and peoples of Israel,
28 Sun taru domin su aiwatar da dukan abin da hannunka da nufinka ya shirya zai faru.
to do whatever Thy hand and Thy counsel did determine before to come to pass.
29 Yanzu, Ya Ubangiji ka dubi kashedin su, ka ba bayin ka ikon furta maganar ka gabagadi.
'And now, Lord, look upon their threatenings, and grant to Thy servants with all freedom to speak Thy word,
30 Sa'adda ka mika hannunka domin warkarwa, alamu da al'ajibai su faru ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
in the stretching forth of Thy hand, for healing, and signs, and wonders, to come to pass through the name of Thy holy child Jesus.'
31 Bayan sun gama addu'a, wurin da suka taru ya girgiza, suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka furta maganar Allah gabagadi.
And they having prayed, the place was shaken in which they were gathered together, and they were all filled with the Holy Spirit, and were speaking the word of God with freedom,
32 Babban taron da suka ba da gaskiya kansu hade yake; kuma ba wanda ya ce da abinda ya mallaka nasa ne; maimakon haka, komai na su daya ne.
and of the multitude of those who did believe the heart and the soul was one, and not one was saying that anything of the things he had was his own, but all things were to them in common.
33 Da iko mai karfi manzannin suka yi shelar shaidarsu game da tashin Yesu Ubangiji daga matattu, babban alheri kuma na bisansu.
And with great power were the apostles giving the testimony to the rising again of the Lord Jesus, great grace also was on them all,
34 Babu wani a cikinsu wanda ya rasa komai, domin masu filaye da gidaje suka sayar suka kawo kudin abin da suka sayar
for there was not any one among them who did lack, for as many as were possessors of fields, or houses, selling [them], were bringing the prices of the thing sold,
35 sai suka kawo kudin gaban manzanni. Aka rarraba wa kowanne mutum bisa ga bukatarsa.
and were laying them at the feet of the apostles, and distribution was being made to each according as any one had need.
36 Yusufu, Balawi, mutumin tsibirin Kubrus, wanda manzannisu ka yi wa lakani da suna Barnaba. (wato, mai karfafa zuciya).
And Joses, who was surnamed by the apostles Barnabas — which is, having been interpreted, Son of Comfort — a Levite, of Cyprus by birth,
37 Yana da fili sai ya sayar da shi ya kawo kudin gaban manzanni.
a field being his, having sold [it], brought the money and laid [it] at the feet of the apostles.

< Ayyukan Manzanni 4 >