< Ayyukan Manzanni 20 >

1 Bayan da rikici ya kare, Bulus ya aika a kira al'majiran, ya karfafa su. Sa'annan ya yi bankwana da su, ya tashi zai tafi Makidoniya.
After the uproar had ceased, Paul sent for the disciples and, after encouraging them, took leave of them, and departed to go into Macedonia.
2 Bayan ya ratsa cikin lardunan yana yi wa masu bi gargadi sosai, sai ya zo kasar Helenawa.
When he had gone through those parts, and had encouraged them with many words, he came into Greece.
3 Sa'adda ya yi wata uku a wurin, Yahudawa suka kulla masa makirci, yayin da yake shirin hawa Jirgi zuwa Suriya, sai ya canza ra'ayi ya koma ta Makidoniya.
When he had spent three months there, and a plot was made against him by Jews as he was about to set sail for Syria, he determined to return through Macedonia.
4 Masu yi wa Bulus rakiyar zuwa yankin Asiya sun hada da Sobatarus dan Burus daga Biriya; Gayus mutumin Derbe; Timoti da Aristakus da Sakundus, dukansu masu bi ne daga Tasalonika; da Tikikus da Trofimus daga Asiya.
He was accompanied by Sopater son of Pyrrhus of Beroea; Aristarchus and Secundus of the Thessalonians; Gaius of Derbe; Timothy; and Tychicus and Trophimus of Asia.
5 Amma wadansu har suka rigaye mu, suka jira mu a Taruwasa.
But these had gone ahead, and were waiting for us at Troas.
6 Da muka shiga Jirgi daga Filibi bayan kwanakin Gurasa mara yisti; bayan kwanaki biyar muka iske su a Taruwasa; kwananmu bakwai a wurin.
We sailed away from Philipus after the days of Unleavened Bread, and came to them at Troas in five days, where we stayed seven days.
7 A rana ta fari ga mako, da muka taru domin karya gurasa. Bulus ya yi wa masubi jawabi, don ya yi niyyar ya tafi da wayewar gari; jawabinsa ya kai har tsakar dare.
On the first day of the week, when we were gathered together to break bread, Paul talked with them, intending to depart on the next day, and continued his speech until midnight.
8 A benen da suka taru akwai fitilu da yawa.
There were many lights in the upper chamber where we were gathered together.
9 Wani matashi mai suna Aftikos yana zaune a kan taga, barci mai nauyi ya dauke shi; da shike Bulus ya tsawaita jawabinsa, saurayin da shike barci mai nauyi ya dauke shi sai ya fado daga kan bene na uku aka dauke shi matacce.
A certain young man named Eutychus sat in the window, weighed down with deep sleep. As Paul spoke still longer, being weighed down by his sleep, he fell down from the third story, and was taken up dead.
10 Sai Bulus ya sauka ya mike a bisansa ya rungume shi, sa'annan ya ce, “Kada kowa ya damu; domin yana darai bai mutu ba.”
Paul went down, and fell upon him, and embracing him said, "Do not be troubled, for his life is in him."
11 Sa'annan ya hawo kan bene domin cin gurasa tare da su, ya yi magana da su har gari ya waye daga nan ya bar su.
When he had gone up, and had broken bread, and eaten, and had talked with them a long while, even until break of day, he departed.
12 Suka kawo saurayin da rai, sun sami ta'aziya ba kadan ba.
They brought the boy in alive, and were greatly comforted.
13 Amma mu, da muka riga Bulus zuwa gun Jirgin, muka shiga zuwa Asos, mun shirya mu dauki Bulus a jirgi amma shi ya kudurta ya yi tafiya a kasa.
But we who went ahead to the ship set sail for Assos, intending to take Paul aboard there, for he had so arranged, intending himself to go by land.
14 Da muka sadu a Asos, mun dauke shi a Jirgin ruwa zuwa Mitilitus.
When he met us at Assos, we took him aboard, and came to Mitylene.
15 Bayan tashin mu daga can, washegari muka zo tsibirin Kiyos. Washegari kuma muka zo birnin Militus.
Sailing from there, we came the following day opposite Chios. The next day we landed at Samos, and the day after we came to Miletus.
16 Amma Bulus ya kudurta wucewa Afisa a Jirgi, don kada ya bata lokaci a Asiya, don yana sauri in ya yiwu ranar Fentekos ta same shi a Urushalima.
For Paul had determined to sail past Ephesus, that he might not have to spend time in Asia; for he was hastening, if it were possible for him, to be in Urishlim on the day of Pentecost.
17 Daga Militus ya aika a kira masa dattawan iklisiyar Afisa.
From Miletus he sent to Ephesus, and called to himself the elders of the church.
18 Da suka zo wurinsa sai ya ce masu, “Ku da kanku kun san tun daga ranar da na sa kafata a Asiya, irin zaman da muka yi da kasancewar mu tare.
When they had come to him, he said to them, "You yourselves know, from the first day that I set foot in Asia, how I was with you all the time,
19 Na bauta wa Ubangiji da tawaliu har da hawaye, da wahalun da na sha saboda makircin Yahudawa.
serving the Lord with all humility, with many tears, and with trials which happened to me by the plots of the Jews;
20 Kun sani ban ji nauyin sanar da ku kowanne abu mai amfani ba, na bi ku gida gida ina koyar da ku abubuwa a sarari.
how I did not hold back from declaring to you anything that was profitable, and teaching you publicly and from house to house,
21 Kunsan yadda na gargadi Yahudawa da Hellenawa game da tuba ga Allah da bangaskiya ga Ubangiji Yesu.
testifying both to Jews and to Greeks repentance toward God, and faith toward our Lord Yeshua.
22 Yanzu fa, gashi, zan tafi Urushalima, Ruhu Mai Tsarki ya nuna mani a fili dole in je, ban san abin da zai faru da ni a can ba.
And now, look, compelled by the Rukha, I am going to Urishlim, not knowing what will happen to me there;
23 Sai dai Ruhu Mai Tsarki ya nuna mani a kowanne gari cewa, sarkoki da wahalu suna jira na.
except that the Rukha d'Qudsha testifies in every city, saying that bonds and afflictions wait for me.
24 Amma ban dauka cewa raina yana da wani amfani gare ni ba, domin in cika tsere da hidimar da na karba daga wurin Ubangiji Yesu, ta shaidar bisharan alherin Allah.
But I make my life an account of nothing precious to myself, so that I may finish my race, and the ministry which I received from the Lord Yeshua, to fully testify to the Good News of the grace of God.
25 Yanzu fa, duba, na san dukanku, wadanda na yi wa wa'azin mulkin Allah, ba za ku kara gani na ba.
"And now, look, I know that you all, among whom I went about proclaiming the Kingdom, will see my face no more.
26 Don haka na shaida maku a wannan rana, ba ni da alhakin jinin kowanne mutum.
Therefore I testify to you today that I am innocent of everyone's blood,
27 Don banji nauyin sanar maku da dukan nufin Allah a gare ku ba.
for I did not hold back from declaring to you the whole plan of God.
28 Saboda haka ku kula da kanku, da masubi da Ruhu Mai Tsarki ya sanya ku shugabanni. Ku kula ku yi kiwon iklisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa.
Watch out for yourselves and to all the flock, in which the Rukha d'Qudsha has made you overseers, to shepherd the church of God which he purchased with his own blood.
29 Na sani cewa bayan tafiyata, kyarketai masu zafi za su shiga tsakaninku, kuma baza su rangwanta wa masubi ba.
For I know that after my departure, vicious wolves will enter in among you, not sparing the flock.
30 Na sani har daga cikinku wadansu mazaje za su zo su fadi gurbattatun zantattuka, domin su janye almajirai zuwa gare su.
Men will arise from among your own selves, speaking perverse things, to draw away the disciples after them.
31 Saboda haka ku yi lura. Ku tuna da cewa shekara uku ban fasa yi wa kowannenku gargadi da hawaye dare da rana ba.
Therefore watch, remembering that for a period of three years I did not cease to admonish everyone night and day with tears.
32 Yanzu ina mika ku ga Allah, da maganar Alherinsa, wadda take da ikon gina ku ta kuma ba ku gado tare da dukan wadanda ke cikin kebabbu na Allah.
Now I entrust you to God, and to the word of his grace, which is able to build up, and to give you the inheritance among all those who are sanctified.
33 Ban yi kyashin azurfa, ko zinariya, ko tufafin wani ba.
I coveted no one's silver, or gold, or clothing.
34 Ku da kanku kun sani na yi aiki da hannuwana, na biya bukatu na da na wadanda ke tare da ni.
You yourselves know that these hands served my necessities, and those who were with me.
35 Na zama maku abin koyi a kowace hanya game da yadda za ku taimaka wa nakasassu ta wurin aiki, da yadda za ku tuna da maganar Ubangiji Yesu, maganar da shi da kansa ya ce: ''Bayarwa tafi karba albarka.''
In all things I gave you an example, that so laboring you ought to help the weak, and to remember the words of the Lord Yeshua, that he himself said, 'It is more blessed to give than to receive.'"
36 Bayan da ya yi magana haka, ya durkusa ya yi addu'a tare da su duka.
When he had spoken these things, he knelt down and prayed with them all.
37 Dukansu kuwa suka yi kuka mai tsannani, suka rungume shi kuma suka sunbace shi.
They all wept a lot, and fell on Paul's neck and kissed him,
38 Suka yi bakin ciki musamman domin abin da ya ce masu, ba za su kara ganinsa ba. Sai dukansu suka yi masa rakiya zuwa wurin jirgin ruwa.
sorrowing most of all because of the word which he had spoken, that they should see his face no more. And they accompanied him to the ship.

< Ayyukan Manzanni 20 >