< Zefaniya 1 >

1 Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata. Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
La parole de Yahweh qui fut adressée à Sophonie, fils de Chusi, fils de Godolias, fils d'Amarias, fils d'Ezéchias, dans les jours de Josias, fils d'Amon, roi de Juda.
2 “Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
J'enlèverai tout de dessus la face de la terre, — oracle de Yahweh;
3 “Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
j'enlèverai les hommes et les bêtes, j'enlèverai les oiseaux du ciel et les poissons de la mer, et les scandales avec les impies, et j'exterminerai l'homme de dessus la face de la terre, — oracle de Yahweh.
4 “Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
Et j'étendrai ma main sur Juda, et sur tous les habitants de Jérusalem, et j'exterminerai de ce lieu le reste de Baal, le nom de ses ministres en même temps que les prêtres;
5 waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
et ceux qui se prosternent sur les toits, devant l'armée des cieux; et ceux qui se prosternent en faisant serment à Yahweh, tout en jurant par leur roi;
6 Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
et ceux qui se détournent de Yahweh, qui ne cherchent pas Yahweh, et ne se soucient pas de lui.
7 Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
Silence devant le Seigneur Yahweh! Car le jour de Yahweh est proche; car Yahweh a préparé un sacrifice, il a consacré ses invités.
8 “A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
Et il arrivera: Au jour du sacrifice de Yahweh, je châtierai les princes, et les fils de roi, et tous ceux qui revêtent des vêtements étrangers.
9 A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
Et je châtierai en ce jour-là tous ceux qui sautent par-dessus le seuil, qui remplissent de violence et de fraude la maison de leur maître.
10 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
Et il arrivera en ce jour-là, — oracle de Yahweh: De la porte des poissons retentiront des cris, de la seconde ville des gémissements, et des collines un grand fracas.
11 Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
Gémissez, habitants du Mortier, car tout le peuple chananéen est anéanti, tous ceux qui sont chargés d'argent sont exterminés.
12 A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
Et il arrivera en ce temps-là: Je fouillerai Jérusalem avec des lanternes, et je châtierai les hommes figés sur leur lie, qui disent en leur cœur: " Yahweh ne fait ni bien ni mal! "
13 Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
Leurs biens seront livrés au pillage, et leurs maisons à la dévastation; ils bâtiront des maisons, et ils n'y habiteront point; ils planteront des vignes, et ils n'en boiront pas le vin.
14 Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
Il est proche le grand jour de Yahweh, il est proche, il vient en toute hâte! On l'entend venir, le jour de Yahweh! L'homme brave y poussera des cris amers.
15 Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
C'est un jour de fureur que ce jour-là, un jour d'angoisse et d'affliction, un jour de désolation et de ruine, un jour de ténèbres et d'obscurité, un jour de nuages et d'épais brouillards,
16 rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
un jour de trompette et d'alarme, sur les villes fortes et les créneaux élevés.
17 “Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
Je mettrai les hommes dans la détresse, et ils marcheront comme des aveugles, parce qu'ils ont péché contre Yahweh; leur sang sera répandu comme la poussière; et leur chair comme du fumier.
18 Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.
Ni leur argent, ni leur or ne pourront les délivrer; au jour de la fureur de Yahweh; par le feu de sa jalousie, toute la terre sera dévorée; car il fera une destruction totale, une ruine soudaine, de tous les habitants de la terre.

< Zefaniya 1 >