< Rut 3 >

1 Wata rana Na’omi surukar Rut ta ce mata, “’Yata, bai kamata in nema miki gida, inda za a tanada miki da kyau?
One day, Naomi said to Ruth, ‘My daughter, should I not seek to secure a home for you where you will be happy and prosperous?
2 Bowaz wanda kike aiki da bayinsa’yan mata ba danginmu ne na kusa ba? Da daren yau zai sussuka sha’ir nasa a masussuka.
Is not Boaz, with whose girls you have been, a relative of ours?
3 Ki yi wanka ki fesa turare, ki kuma sa tufafinki mafi kyau. Sa’an nan ki gangara zuwa masussuka, amma kada ki bari yă san cewa kina a can sai ya gama ci da sha.
Tonight he is going to winnow barley on the threshing-floor. So bathe and anoint yourself and put on your best clothes and go down to the threshing-floor. But do not make yourself known to the man until he has finished eating and drinking.
4 Sa’ad da ya kwanta, ki lura da inda yake kwance. Sa’an nan ki tafi ki buɗe ƙafafunsa ki kwanta. Zai faɗa miki abin da za ki yi.”
Then when he lies down, mark the place where he lies. Go in, uncover his feet, lie down, and then he will tell you what to do.’
5 Rut ta amsa ta ce “Zan yi abin da kika faɗa.”
‘I will do as you say.’ Ruth said to her.
6 Saboda haka ta gangara zuwa masussuka ta kuma yi dukan abin da surukarta ta ce ta yi.
So she went down to the threshing-floor and did just as her mother-in-law told her.
7 Sa’ad da Bowaz ya gama ci da sha yana kuma cikin farin ciki, sai ya tafi ya kwanta a ƙarshen tarin hatsi. Rut kuwa ta sulalle ta je ta buɗe ƙafafunsa ta kwanta.
When Boaz had finished eating and drinking and was in a happy mood, he went to lie down at the end of the heap of grain. Then Ruth came quietly and uncovered his feet and lay down.
8 Da tsakar dare sai wani abu ya firgitar da mutumin, ya kuwa juya sai ya tarar da mace kwance a ƙafafunsa.
At midnight the man was startled and turned over, and there was a woman lying at his feet!
9 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ke wace ce?” Ta amsa ta ce, “Ni ce baranyarka Rut, ka rufe ni ta mayafinka da yake kai dangi, mai fansa ne na kusa.”
‘Who are you?’ he said. ‘I am Ruth your servant,’ she answered, ‘Spread your cloak over your servant, for you are a near relative.’
10 Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji yă albarkace ki’yata. Wannan alheri ya fi wannan da kika nuna da farko. Ba ki gudu kin bi saurayi, mai arziki ko matalauci ba.
He said, ‘May you be blest by the Lord, my daughter. You have shown me greater favour now than at first, for you have not followed young men, whether poor or rich.
11 Yanzu kuwa’yata kada ki ji tsoro. Zan yi miki dukan abin da kika roƙa. Dukan’yan’uwana na gari sun san cewa ke mace ce mai halin kirki.
My daughter, have no fear. I will do for you all that you ask, for the whole town knows that you are a virtuous woman.
12 Ko da yake gaskiya ne ni dangi ne na kusa, amma akwai dangi mai fansa mafi kusa fiye da ni.
Now it is true that I am a near relative, but there is another man nearer than I.
13 Ki kwana a nan, da safe kuwa in yana so yă fansa, to, da kyau, sai yă fansa. Amma in ba ya niyya, tabbatacce, na rantse da Ubangiji mai rai zan yi. Ki kwanta a nan sai da safe.”
Stay here tonight, and then in the morning, if he will perform for you the duty of a kinsman, well, let him do it. But if he will not perform for you the duty of a kinsman, then as surely as the Lord lives, I will do it for you. Lie down until morning.’
14 Saboda haka ta kwanta a ƙafafunsa sai da safe, amma ta tashi kafin a gane wani, sai ya ce, “Kada ki bar wani yă san cewa mace ta zo masussuka.”
So she lay at his feet until morning, but rose before anyone could recognise her, for Boaz said, ‘No one must know that a woman came to the threshing-floor.’
15 Ya kuma ce, “Ki kawo gyalenki da kika yafa ki shimfiɗa shi a nan.” Sa’ad da ta yi haka, sai ya zuba mudu shida na sha’ir ya sa mata a kai. Sa’an nan ya koma gari.
He also said, ‘Bring the cloak which you have on and hold it.’ So she held it while he poured into it six measures of barley and laid it on her shoulders. Then he went into the city.
16 Sa’ad da Rut ta koma wurin surukarta Na’omi ta tambaye ta “Yaya aka yi’yata?” Sai ta faɗa mata dukan abin da Bowaz ya yi mata
When Ruth came to her mother-in-law, Naomi asked, ‘Is it you, my daughter?’ Then Ruth told Naomi all that the man had done for her.
17 ta kuma ƙara da cewa, “Ya ba ni waɗannan mudu shida na sha’ir, yana cewa, ‘Kada ki koma wurin surukarki hannu wofi.’”
‘He gave me these six measures of barley,’ she said, ‘for he said I should not go to my mother-in-law empty-handed.’
18 Sai Na’omi ta ce, “Ki jira,’yata, sai kin ga abin da zai faru. Gama mutumin ba zai huta ba sai an warware batun a yau.”
‘Wait quietly, my daughter.’ Naomi said, ‘Until you know how the affair will turn out, for the man will not rest unless he settles it all today.’

< Rut 3 >