< Romawa 10 >

1 ’Yan’uwa, abin da zuciyata take so da kuma addu’ata ga Allah saboda Isra’ilawa shi ne su sami ceto.
Brothers, my heart’s desire and prayer to God for my People is for their Salvation.
2 Gama na shaida su a kan suna da kishi bin Allah, sai dai kishinsu ba a bisa sani ba.
I can testify that they are zealous for the honour of God; but they are not guided by true insight,
3 Da yake ba su san adalcin da yake fitowa daga Allah ba suka kuma nemi su kafa nasu, sai suka ƙi miƙa kai ga adalcin Allah.
for, in their ignorance of the Divine Righteousness, and in their eagerness to set up a righteousness of their own, they refused to accept with submission the Divine Righteousness.
4 Kiristi shi ne ƙarshen doka domin a sami adalci wa kowane mai bangaskiya.
For Christ has brought Law to an end, so that righteousness may be obtained by every one who believes in him.
5 Musa ya bayyana adalcin da yake ga Doka cewa, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
For Moses writes that, as for the righteousness which results from Law, ‘those who practice it will find Life through it.’
6 Amma adalcin da yake ga bangaskiya yana cewa, “Kada ka faɗa a zuciyarka, ‘Wa zai hau sama?’” (wato, don yă sauko da Kiristi),
But the righteousness which results from faith finds expression in these words — ‘Do not say to yourself “Who will go up into heaven?”’ — which means to bring Christ down —
7 “ko kuwa ‘Wa zai gangara can zurfin ƙasa?’” (wato, don yă hauro da Kiristi daga matattu). (Abyssos g12)
‘or “Who will go down into the depths below?”’ — which means to bring Christ up from the dead. (Abyssos g12)
8 Amma mene ne aka ce? “Maganar tana kusa da kai; tana cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka,” wato, maganar bangaskiyan nan da muke shela.
No, but what does it say? ‘The Message of Faith’ which we proclaim.
9 Cewa in ka furta da bakinka, “Yesu Ubangiji ne,” ka kuma gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tā da shi daga matattu, za ka sami ceto.
For, if with your lips you acknowledge the truth of the Message that JESUS IS LORD, and believe in your heart that God raised him from the dead, you shall be saved.
10 Gama da zuciyarka ce kakan gaskata a kuma kuɓutar da kai, da bakinka ne kuma kake furta a kuma cece ka.
For with their hearts men believe and so attain to righteousness, while with their lips they make their Profession of Faith and so find Salvation.
11 Kamar yadda Nassi ya ce, “Duk wanda ya gaskata da shi ba zai taɓa shan kunya ba.”
As the passage of Scripture says — ‘No one who believes in him shall have any cause for shame.’
12 Gama ba bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, Ubangijin nan ɗaya shi ne Ubangijin kowa yana kuma ba da albarka a yalwace ga duk masu kira gare shi,
For no distinction is made between the Jew and the Greek, for all have the same Lord, and he is bountiful to all who invoke him.
13 gama, “Duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.”
For ‘every one who invokes the Name of the Lord shall be saved.’
14 To, ta yaya za su kira ga wanda ba su gaskata ba? Ta yaya kuma za su gaskata wanda ba su taɓa ji ba? Ta yaya kuma za su ji ba tare da wani ya yi musu wa’azi ba?
But how, it may be asked, are they to invoke one in whom they have not learned to believe? And how are they to believe in one whose words they have not heard? And how are they to hear his words unless some one proclaims him?
15 Kuma ta yaya za su yi wa’azi in ba an aike su ba? Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Isowar masu kawo labari mai daɗi abu mai kyau ne ƙwarai!”
And how are men to proclaim him unless they are sent as his messengers? As Scripture says — ‘How beautiful are the feet of those who bring good news!’
16 Amma ba dukan Isra’ilawa ne suka karɓi labari mai daɗin nan ba. Gama Ishaya ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu?”
Still, it may be said, every one did not give heed to the Good News. No, for Isaiah asks — ‘Lord, who has believed our teaching?’
17 Saboda haka, bangaskiya takan zo ne ta wurin jin saƙo, akan ji saƙon kuma ta wurin maganar Kiristi.
And so we gather, faith is a result of teaching, and the teaching comes in the Message of Christ.
18 Amma ina tambaya, “Ba su ji ba ne? Tabbatacce sun ji. “Muryarsu ta tafi ko’ina a cikin duniya, kalmominsu kuma har iyakar duniya.”
But I ask ‘Is it possible that men have never heard?’ No, indeed, for — ‘Their voices spread through all the earth, and their Message to the very ends of the world.’
19 Har wa yau, ina da tambaya. Shin, Isra’ila ba su fahimta ba ne? Da farko, Musa ya ce, “Zan sa ku yi kishin waɗanda ba al’umma ba; zan sa ku yi fushin al’ummar da ba ta da fahimta.”
But again I ask ‘Did not the people of Israel understand? First there is Moses, who says — ‘I, the Lord, will stir you to rivalry with a nation which is no nation; Against an undiscerning nation I will arouse your anger.’
20 Ishaya kuma ya fito gabagadi ya ce, “Waɗanda ba su neme ni ba, su suka same ni; Na bayyana kaina ga waɗanda ba su ma taɓa neman sanina ba.”
And Isaiah says boldly — ‘I was found by those who were not seeking me; I made myself known to those who were not inquiring of me.
21 Amma game da Isra’ila ya ce, “Dukan yini na miƙa hannuwana ga mutane marasa biyayya da masu taurinkai.”
But of the people of Israel he says — ‘All day long I have stretched out my hands to a people who disobey and contradict.’

< Romawa 10 >