< Ru’uya ta Yohanna 2 >

1 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Afisa, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomi na wannan wanda yake riƙe da taurari bakwai a hannunsa na dama yana kuma tafiya a tsakanin alkukan fitilu bakwai na zinariya.
До ангола Церкви в Ефе́сі напиши: „Оце каже Той, Хто трима́є сім зір у правиці Своїй, Хто ходить серед семи світильників золотих:
2 Na san ayyukanka, faman aikinka da daurewarka. Na san cewa ba ka iya haƙuri da mugayen mutane, ka gwada waɗanda suke cewa su manzanni ne, alhali kuwa ba haka ba ne, ka kuwa tarar cewa su na ƙarya ne.
Я знаю діла твої, і працю твою, і твою терпеливі́сть, і що не можеш терпіти лихих, і ви́пробував тих, хто себе називає апо́столами, але ними не є, і знайшов, що фальшиві вони.
3 Kai kam ka daure ka kuma jimre da wahala saboda sunana, ba ka kuwa gaji ba.
І ти маєш терпіння, і працюва́в для Йме́ння Мого, але не знемігся.
4 Duk da haka ina riƙe da wannan game da kai. Ka watsar da ƙaunarka ta farko.
Але маю на тебе, що ти покинув свою першу любов.
5 Ka tuna da matsayinka a dā kafin ka fāɗi! Ka tuba ka kuma yi ayyukan da ka yi da fari. In ba ka tuba ba, zan zo wajenka in ɗauke wurin ajiye fitilanka daga inda yake.
Отож, пам'ятай, звідки ти впав, і покайся, і вчинки давніші роби. Коли ж ні, то до тебе прийду́ незаба́ром, і зру́шу твого світильника́ з його місця, якщо не покаєшся.
6 Sai dai kana da wannan abu mai kyau. Ka ƙi ayyukan Nikolaitawa da ni ma nake ƙi.
Але маєш оце, що нена́видиш учинки Николаї́тів, яких і Я нена́виджу.
7 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ikon ci daga itacen rai, da yake cikin aljannar Allah.
Хто має вухо, хай чує, що Дух промовляє Церква́м: переможцеві дам їсти від дерева життя, яке в раю́ Божім“.
8 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Simirna, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin wannan da yake na Farko da na Ƙarshe, wanda ya mutu ya kuma sāke tashi da rai.
А до ангола Церкви в Смірні напиши: „Оце каже Перший й Останній, що був мертвий й ожив:
9 Na san wahalarka da kuma talaucinka, duk da haka kai mai arziki ne! Na san ɓata suna da waɗannan suke yi maka waɗannan da suke cewa su Yahudawa ne alhali kuwa ba haka ba ne, su dai majami’ar Shaiɗan ne.
Я знаю діла твої, і біду́, і убозтво, — але ти багатий, — і зневагу тих, що говорять про себе, ніби юдеї вони, та ними не є, але вони — зборище сатани.
10 Kada ka ji tsoron wahalar da kake gab da sha. Ina gaya maka, Iblis zai sa waɗansunku a kurkuku don yă gwada ku. Za ku sha tsanani na kwana goma. Ka yi aminci ko da za a kashe ka, ni kuwa zan ba ka rawanin rai.
Не бійся того, що маєш страждати! Ось диявол вкидатиме декого з вас до в'язниць, щоб вас ви́пробувати. І будете мати біду́ десять день. Будь вірний до смерти, і Я тобі дам вінця́ життя!
11 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara mutuwa ta biyu ba za tă cuce shi ba ko kaɗan.
Хто має вухо, хай чує, що́ Дух промовляє Церква́м: переможець не буде пошко́джений від другої смерти“.
12 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Fergamum, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin wannan wanda yake da takobi mai kaifi biyu.
А до ангола Церкви в Перга́мі напиши: „Оце каже Той, що має меча обосі́чного:
13 Na san inda kake da zama, inda Shaiɗan yana da gadon sarautarsa. Duk da haka ka riƙe sunana da gaske. Ba ka yi mūsun bangaskiyarka gare ni ba, har ma a kwanakin Antifas, amintaccen mashaidina, wanda aka kashe a birninku, inda Shaiɗan yake zama.
Я знаю діла твої, і що де ти живеш, там престол сатани. І трима́єш ти Йме́ння Моє, і ти не відкинувся від віри Моєї навіть за днів, коли в вас, де живе сатана́, був убитий Анти́па, свідок Мій вірний.
14 Duk da haka, ina da abubuwa kima game da kai. Kana da mutane a can waɗanda suke riƙe da koyarwar Bala’am, wanda ya koya wa Balak yă ja hankalin Isra’ilawa su yi zunubi ta wurin cin abincin da aka miƙa wa gumaka hadaya, su kuma yi fasikanci.
Але трохи Я маю на тебе, бо маєш там тих, хто трима́ється науки Валаа́ма, що навчав був Бала́ка покласти спотика́ння перед синами Ізраїля, щоб їли ідольські жертви й розпу́сту чинили.
15 Haka ma kana da waɗanda suke riƙe da koyarwar Nikolaitawa.
Так маєш і ти таких, що трима́ються науки Николаїтської так само.
16 Saboda haka ka tuba! In ba haka ba, zan zo wajenka ba da daɗewa ba in yaƙe su da takobin bakina.
Тож покайся! Коли ж ні, то до тебе прийду́ незаба́ром, і воюватиму з ними мечем Своїх уст.
17 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara zan ba shi kaɗan daga cikin ɓoyayyiyar Manna. Zan kuma ba shi farin dutse tare da sabon suna a rubuce a bisansa, sananne kawai ga mai karɓan dutsen.
Хто має вухо, хай чує, що́ Дух промовляє Церква́м: переможцеві дам їсти прихо́вану манну, і дам йому білого каменя, а на камені написане ймення нове́, якого не знає ніхто, — тільки той, хто приймає його“.
18 “Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Tiyatira, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin Ɗan Allah, wanda idanunsa suna kama da harshen wuta wanda kuma ƙafafunsa suna kama da tagullar da aka goge.
І до ангола Церкви в Тіяти́рах напиши: „Оце каже Син Божий, що має очі Свої, як по́лум'я огняне́, а ноги Його подібні до міді:
19 Na san ayyukanka, ƙaunarka da bangaskiyarka, hidimarka da daurewarka, kuma cewa kana yin abubuwa a yanzu fiye da abin da ka yi da farko.
Я знаю діла твої, і любов, і віру, і службу, і твою терпеливість, і останні вчинки твої, що більші за перші.
20 Duk da haka, ina da wannan game da kai. Kana haƙuri da matan nan Yezebel, wadda take kira kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta tana ɓad da bayina ga yin fasikanci suka kuma ci abincin da aka miƙa wa gumaka.
Але маю на тебе, що жінці Єзаве́лі, яка каже, ніби вона пророки́ня, ти попускаєш навчати та зводити рабів Моїх, чинити розпусту та їсти і́дольські жертви.
21 Na ba ta lokaci tă tuba daga fasikancinta, amma ba ta da niyya.
І Я дав був їй ча́су, щоб пока́ялася, — та вона не схотіла покаятися в розпусті своїй.
22 Don haka zan jefa ta a kan gadon wahala, zan kuma sa waɗanda suke zina da ita, su sha azaba ƙwarai, sai dai in sun tuba daga hanyoyinta.
Ось Я кину її на ложе, а тих, що чинять із нею розпусту, у велику біду, коли тільки в учинках своїх не покаються,
23 Zan kashe’ya’yanta. Sa’an nan dukan ikkilisiyoyi za su san cewa ni ne mai bincika zukata da tunani, zan kuwa sāka wa kowannenku gwargwadon ayyukansa.
а діти її поб'ю́ смертю. І пізнають усі Церкви́, що Я Той, Хто нирки й серця вивіря́є, і Я кожному з вас дам за вчинками вашими.
24 Yanzu, ina ce wa sauranku da kuke a Tiyatira, ku da ba ku riƙe da koyarwarta ba kuma ba ku koyi abin da suke kira zurfafan asiran Shaiɗan, ‘Ba zan ƙara muku wani nauyi ba.
А вам, та іншим, що в Тіяти́рах, що не мають науки цієї, і — як кажуть — не розуміють так зва́них глиби́н сатани́, кажу́: не накладу́ на вас іншого тягара,
25 Sai dai ku riƙe abin da kuke da shi har sai na zo.’
тільки те, що ви маєте, трима́йте, аж поки прийду́.
26 Gare shi wanda ya ci nasara ya kuma aikata nufina har ƙarshe, zan ba shi iko a kan al’ummai.
А переможцеві, і тому́, хто аж до кінця доде́ржує Мої вчинки, Я дам йому вла́ду „над поганами,
27 ‘Zai yi mulki a kansu da sandar sarauta ta ƙarfe, zai farfashe su, kamar tukwanen yumɓu’kamar yadda na karɓi iko daga Ubana.
і буде пасти́ їх залізним жезлом; вони, немов гли́няний по́суд, покру́шаться“, як і Я оде́ржав вла́ду від Свого́ Отця,
28 Zan kuma ba shi tauraron asubahi.
і дам Я йому зо́рю досві́тню.
29 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.
Хто має вухо, хай чує, що́ Дух промовляє Церква́м!“

< Ru’uya ta Yohanna 2 >