< Zabura 9 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
Au maître-chantre. — Sur «Meurs pour le fils». — Psaume de David. Je glorifierai l'Éternel de tout mon coeur; Je raconterai toutes ses merveilles.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
Je m'égaierai, je me réjouirai en toi; Je chanterai ton nom, ô Dieu Très-Haut!
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
Car mes ennemis reculent; Ils tombent et périssent devant ta face.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
Oui, tu as soutenu mon droit, tu as défendu ma cause; Tu t'es assis sur ton trône en juste juge.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
Tu as réprimandé les nations, tu as fait périr les méchants; Tu as effacé leur nom pour toujours, à perpétuité.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
Plus d'ennemis. Des ruines éternelles! Tu as détruit leurs villes, Et leur souvenir a péri avec eux.
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
L'Éternel règne à jamais; Il a dressé son trône pour le jugement.
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
Il jugera le monde avec justice; Il jugera les peuples avec équité.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
L'Éternel sera le refuge de l'opprimé, Son refuge au temps de la détresse.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
Ceux qui connaissent ton nom se confieront en toi; Car tu n'abandonnes jamais ceux qui te cherchent, ô Éternel.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Chantez en l'honneur de l'Éternel qui habite en Sion; Annoncez parmi les peuples ses actions glorieuses!
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
Car il se souvient du sang versé, pour en tirer vengeance; Il n'oublie pas le cri des affligés.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Aie pitié de moi, ô Éternel! Vois la détresse où m'ont réduit mes ennemis, toi qui me fais remonter des portes de la mort,
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
Afin que je publie toutes tes louanges Aux portes de la fille de Sion, Et que je me réjouisse du salut que tu m'as accordé.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
Les nations sont tombées dans la fosse qu'elles avaient creusées; Leur pied s'est pris au piège qu'elles avaient caché.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
L'Éternel s'est fait connaître, il a manifesté sa justice: Le méchant a été enlacé dans son propre filet. (Jeu d'instruments, Pause)
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
Les méchants s'en vont au Séjour des morts, Avec toutes les nations qui oublient Dieu. (Sheol h7585)
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
Le malheureux ne sera pas toujours oublié, Et l'espoir des opprimés ne sera pas éternellement trompé.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Lève-toi, ô Éternel! Que l'homme ne triomphe pas. Que les nations soient jugées devant ta face!
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Éternel, répands sur elles la frayeur: Que les peuples sachent qu'ils ne sont que des hommes! (Pause)

< Zabura 9 >