< Zabura 88 >

1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
[Psalm Lun Tulik Natul Korah; Ac Heman, Mwet Ezra] O LEUM GOD su langoeyu, nga wowoyak ac tung len fon, Ac ke fong nga tuku nu ye motom.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Lohng pre luk, Lipsre tung luk in suk kasru!
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
Tuh mwe keok puspis putati nu fuk Ac nga apkuran in misa. (Sheol h7585)
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
Nga oana elos nukewa su apkuran in misa; Wanginla ku luk.
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Sisila nga inmasrlon mwet misa, Nga oana mwet su anwuki ac pukpuki in kulyuk uh — Oana elos su kom tiana sifil esam, Su kom fah tia ku in sifilpa kasru.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Kom sisyula nu in lufin mas loallana, Nu in luf se su arulana lohsr ac loal.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Mulat lom putati toasr nu fuk Ac nga itungyuki ye noa in kasrkusrak lom.
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Kom oru tuh mwet kawuk luk in sisyula, Ac oru tuh nga in oana mwe srungayuk selos. Nga kauli ac tia ku in kaingkunla.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Mutuk losrla ke keok luk, LEUM GOD, nga sralak pouk Ac pre nu sum len nukewa.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Ya kom ac oru ma sakirik usrnguk nu sin mwet misa? Ya elos ac tukakek ac kaksakin kom?
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Ya lungse kawil lom srumunyuk in kulyuk uh? Ya oaru lom srumunyuk ke acn in kunausten?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Ya mwenmen lom liyeyuk in acn lohsr uh, Ku wo lom liyeyuk ke acn sin mwet mulkinyukla uh?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
LEUM GOD, nga pre nu sum in kasreyu. Nga pre nu sum ke lotutang nukewa.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Efu ku kom sisyula, LEUM GOD? Efu ku kom ngetla likiyu?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
Nga nuna keok ac apkuran nu ke misa e ke nga srikyak, Nga totola ke ma toasr su kom kaiyu kac.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Mulat upa lom itungyuwi — Mwe aksangeng lom kunausyula.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
Ma inge apinyula oana sronot ke len nufon, Ac kuhlusyuwi ke siska nukewa.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Finne kawuk fototo luk, kom oru elos sisyula, Ac lohsr mukena pa nga liye uh.

< Zabura 88 >