< Zabura 86 >

1 Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
Una oración de David. ¡Señor, por favor escúchame! ¡Por favor, respóndeme, porque soy débil y necesito tu ayuda!
2 Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
No me dejes morir, porque yo soy fiel a ti. Sálvame, porque soy tu siervo y confío en ti. Tú eres mi Dios.
3 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
Sé bondadoso conmigo, Señor, porque clamo a ti todo el día.
4 Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
Hazme feliz, Señor, porque he dedicado mi vida a ti.
5 Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
Porque tú, Señor, eres bueno; tú eres perdonador y amoroso con todos los que vienen a ti.
6 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
Señor, por favor, escucha mi oración. Escucha mi clamor a ti pidiendo ayuda.
7 A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
Cuando estoy en problemas clamo a ti porque sé que me responderás.
8 A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
Señor, no hay nadie como tú entre los “dioses”. Nadie puede hacer las cosas que tú haces.
9 Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
Tú creaste todas las naciones, y estas vendrán y se postrarán delante de ti. Declararán cuán maravilloso eres.
10 Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
¡Porque tú eres grande, y haces grandes cosas! Solo tú eres Dios.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
Señor, enséñame tus caminos, para que pueda depender de ti. Hazme leal, para que pueda honrarte.
12 Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
Dios mío, Te agradezco desde los más profundo de mi corazón. Te alabaré por siempre.
13 Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
Porque tu amor es grande para mí; me has salvado de la muerte. (Sheol h7585)
14 Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
Dios, gente arrogante me está atacando.
15 Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
Pero tú, Señor, eres un Dios compasivo y lleno de gracia, lento para la ira, lleno de amor y fidelidad.
16 Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
Vuélvete a mí, ten misericordia conmigo. Dale tu fuerza a tu siervo; salva al hijo de tu criada.
17 Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.
¡Muéstrame una señal de que me apruebas! Los que me odian la verán, y serán avergonzados porque tú, Señor, me has ayudado.

< Zabura 86 >