< Zabura 79 >

1 Zabura ta Asaf. Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka; sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki, sun bar Urushalima kufai.
Psaume d'Asaph. O Dieu, les nations ont envahi ton héritage, elles ont profané ton saint temple, elles ont fait de Jérusalem un monceau de pierres.
2 Sun ba da gawawwakin bayinka kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama, nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.
Elles ont livré les cadavres de tes serviteurs en pâture aux oiseaux du ciel, et la chair de tes fidèles aux bêtes de la terre.
3 Sun zubar da jini kamar ruwa ko’ina a Urushalima, kuma babu wani da zai binne matattu.
Elles ont versé leur sang comme de l'eau, tout autour de Jérusalem, et personne pour leur donner la sépulture!
4 Mun zama abin reni ga maƙwabta, abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Nous sommes devenus un objet d'opprobre pour nos voisins, de risée et de moquerie pour ceux qui nous entourent.
5 Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne? Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?
Jusques à quand, Yahweh, seras-tu irrité pour toujours, et ta colère s'allumera-t-elle comme le feu?
6 Ka zuba fushinka a kan al’umman da ba su yarda da kai ba, a kan mulkokin da ba sa kira bisa sunanka;
Répands ta fureur sur les nations qui ne te connaissent pas, sur les royaumes qui n'invoquent pas ton nom.
7 gama sun cinye Yaƙub suka lalatar da ƙasar zamansa.
Car ils ont dévoré Jacob, et ravagé sa demeure.
8 Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu; bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu, gama mun fid da zuciya sarai.
Ne te souviens plus contre nous des iniquités de nos pères; que ta compassion vienne en hâte au-devant de nous, car notre misère est au comble.
9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, saboda ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu saboda sunanka.
Secours-nous, Dieu de notre salut, pour la gloire de ton nom, délivre-nous et pardonne nos péchés à cause de ton nom.
10 Don me al’ummai za su ce, “Ina Allahnsu yake?” A idanunmu, ka sanar wa al’ummai cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.
Pourquoi les nations diraient-elles: " Où est leur Dieu? " Qu'on connaisse parmi les nations, et sous nos yeux, la vengeance que tu tires du sang de tes serviteurs, quand il est répandu!
11 Bari nishe-nishen’yan kurkuku su zo gabanka; ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.
Que les gémissements des captifs montent jusqu'à toi; selon la grandeur de ton bras, sauve ceux qui vont périr!
12 Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.
Fais retomber sept fois dans le sein de nos voisins les outrages qu'ils t'ont faits, Seigneur!
13 Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka, za mu yabe ka har abada; daga tsara zuwa tsara za mu yi ta ba da labarin yabonka.
Et nous, ton peuple, le troupeau de ton pâturage, nous te rendrons gloire à jamais; d'âge en âge, nous publierons tes louanges.

< Zabura 79 >