< Zabura 79 >

1 Zabura ta Asaf. Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka; sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki, sun bar Urushalima kufai.
A Psalm of Asaph. O God, the heathen are come into thine inheritance; thy holy temple have they defiled; they have laid Jerusalem on heaps.
2 Sun ba da gawawwakin bayinka kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama, nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.
The dead bodies of thy servants have they given [to be] meat unto the fowls of the heaven, the flesh of thy saints unto the beasts of the earth.
3 Sun zubar da jini kamar ruwa ko’ina a Urushalima, kuma babu wani da zai binne matattu.
Their blood have they shed like water round about Jerusalem; and [there was] none to bury [them].
4 Mun zama abin reni ga maƙwabta, abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
We are become a reproach to our neighbours, a scorn and derision to them that are round about us.
5 Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne? Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?
How long, LORD? wilt thou be angry for ever? shall thy jealousy burn like fire?
6 Ka zuba fushinka a kan al’umman da ba su yarda da kai ba, a kan mulkokin da ba sa kira bisa sunanka;
Pour out thy wrath upon the heathen that have not known thee, and upon the kingdoms that have not called upon thy name.
7 gama sun cinye Yaƙub suka lalatar da ƙasar zamansa.
For they have devoured Jacob, and laid waste his dwelling place.
8 Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu; bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu, gama mun fid da zuciya sarai.
O remember not against us former iniquities: let thy tender mercies speedily prevent us: for we are brought very low.
9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, saboda ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu saboda sunanka.
Help us, O God of our salvation, for the glory of thy name: and deliver us, and purge away our sins, for thy name’s sake.
10 Don me al’ummai za su ce, “Ina Allahnsu yake?” A idanunmu, ka sanar wa al’ummai cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.
Wherefore should the heathen say, Where [is] their God? let him be known among the heathen in our sight [by] the revenging of the blood of thy servants [which is] shed.
11 Bari nishe-nishen’yan kurkuku su zo gabanka; ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.
Let the sighing of the prisoner come before thee; according to the greatness of thy power preserve thou those that are appointed to die;
12 Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.
And render unto our neighbours sevenfold into their bosom their reproach, wherewith they have reproached thee, O Lord.
13 Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka, za mu yabe ka har abada; daga tsara zuwa tsara za mu yi ta ba da labarin yabonka.
So we thy people and sheep of thy pasture will give thee thanks for ever: we will shew forth thy praise to all generations.

< Zabura 79 >