< Zabura 79 >

1 Zabura ta Asaf. Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka; sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki, sun bar Urushalima kufai.
A Psalm by Asaph. God, the nations have come into your inheritance. They have defiled your holy temple. They have laid Jerusalem in heaps.
2 Sun ba da gawawwakin bayinka kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama, nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.
They have given the dead bodies of your servants to be food for the birds of the sky, the flesh of your saints to the animals of the earth.
3 Sun zubar da jini kamar ruwa ko’ina a Urushalima, kuma babu wani da zai binne matattu.
They have shed their blood like water around Jerusalem. There was no one to bury them.
4 Mun zama abin reni ga maƙwabta, abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
We have become a reproach to our neighbors, a scoffing and derision to those who are around us.
5 Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne? Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?
How long, LORD? Will you be angry forever? Will your jealousy burn like fire?
6 Ka zuba fushinka a kan al’umman da ba su yarda da kai ba, a kan mulkokin da ba sa kira bisa sunanka;
Pour out your wrath on the nations that do not know you, on the kingdoms that do not call on your name,
7 gama sun cinye Yaƙub suka lalatar da ƙasar zamansa.
for they have devoured Jacob, and destroyed his homeland.
8 Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu; bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu, gama mun fid da zuciya sarai.
Do not hold the iniquities of our forefathers against us. Let your tender mercies speedily meet us, for we are in desperate need.
9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, saboda ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu saboda sunanka.
Help us, God of our salvation, for the glory of your name. Deliver us, and forgive our sins, for your name’s sake.
10 Don me al’ummai za su ce, “Ina Allahnsu yake?” A idanunmu, ka sanar wa al’ummai cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.
Why should the nations say, “Where is their God?” Let it be known among the nations, before our eyes, that vengeance for your servants’ blood is being poured out.
11 Bari nishe-nishen’yan kurkuku su zo gabanka; ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.
Let the sighing of the prisoner come before you. According to the greatness of your power, preserve those who are sentenced to death.
12 Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.
Pay back to our neighbors seven times into their bosom their reproach with which they have reproached you, Lord.
13 Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka, za mu yabe ka har abada; daga tsara zuwa tsara za mu yi ta ba da labarin yabonka.
So we, your people and sheep of your pasture, will give you thanks forever. We will praise you forever, to all generations.

< Zabura 79 >