< Zabura 70 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Roƙo. Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
To the chief Musician. [A Psalm] of David: to bring to remembrance. Make haste, O God, to deliver me; Jehovah, [hasten] to my help.
2 Bari masu neman raina su sha kunya su kuma rikice; bari dukan masu sha’awar gani lalacewata su juye baya da kunya.
Let them be ashamed and brought to confusion that seek after my soul; let them be turned backward and confounded that take pleasure in mine adversity;
3 Bari masu ce mini, “Allah yă ƙara!” Su juye baya saboda kunyansu.
Let them turn back because of their shame that say, Aha! Aha!
4 Amma bari dukan masu nemanka su yi farin ciki su kuma yi murna a cikinka; bari waɗanda suke ƙaunar cetonka kullum su ce, “Bari Allah yă sami ɗaukaka!”
Let all those that seek thee be glad and rejoice in thee, and let such as love thy salvation say continually, Let God be magnified!
5 Duk da haka ni matalauci ne da kuma mai bukata; ka zo da sauri gare ni, ya Allah. Kai ne mai taimakona da mai cetona; Ya Ubangiji, kada ka yi jinkiri.
But I am afflicted and needy: make haste unto me, O God. Thou art my help and my deliverer: O Jehovah, make no delay.

< Zabura 70 >