< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
To the chief Musician upon Shoshannim, [A Psalm] of David. Save me, O God; for the waters are come in unto [my] soul.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
I sink in deep mire, where [there is] no standing: I am come into deep waters, where the floods overflow me.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
I am weary of my crying: my throat is dried: mine eyes fail while I wait for my God.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
They that hate me without a cause are more than the hairs of mine head: they that would destroy me, [being] mine enemies wrongfully, are mighty: then I restored [that] which I took not away.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
O God, thou knowest my foolishness; and my sins are not hid from thee.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Let not them that wait on thee, O Lord GOD of hosts, be ashamed for my sake: let not those that seek thee be confounded for my sake, O God of Israel.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Because for thy sake I have borne reproach; shame hath covered my face.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
I am become a stranger unto my brethren, and an alien unto my mother’s children.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
For the zeal of thine house hath eaten me up; and the reproaches of them that reproached thee are fallen upon me.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
When I wept, [and chastened] my soul with fasting, that was to my reproach.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
I made sackcloth also my garment; and I became a proverb to them.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
They that sit in the gate speak against me; and I [was] the song of the drunkards.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
But as for me, my prayer [is] unto thee, O LORD, [in] an acceptable time: O God, in the multitude of thy mercy hear me, in the truth of thy salvation.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Deliver me out of the mire, and let me not sink: let me be delivered from them that hate me, and out of the deep waters.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Let not the waterflood overflow me, neither let the deep swallow me up, and let not the pit shut her mouth upon me.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Hear me, O LORD; for thy lovingkindness [is] good: turn unto me according to the multitude of thy tender mercies.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
And hide not thy face from thy servant; for I am in trouble: hear me speedily.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Draw nigh unto my soul, [and] redeem it: deliver me because of mine enemies.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Thou hast known my reproach, and my shame, and my dishonour: mine adversaries [are] all before thee.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Reproach hath broken my heart; and I am full of heaviness: and I looked [for some] to take pity, but [there was] none; and for comforters, but I found none.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
They gave me also gall for my meat; and in my thirst they gave me vinegar to drink.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Let their table become a snare before them: and [that which should have been] for [their] welfare, [let it become] a trap.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Let their eyes be darkened, that they see not; and make their loins continually to shake.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Pour out thine indignation upon them, and let thy wrathful anger take hold of them.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Let their habitation be desolate; [and] let none dwell in their tents.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
For they persecute [him] whom thou hast smitten; and they talk to the grief of those whom thou hast wounded.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Add iniquity unto their iniquity: and let them not come into thy righteousness.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Let them be blotted out of the book of the living, and not be written with the righteous.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
But I [am] poor and sorrowful: let thy salvation, O God, set me up on high.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
I will praise the name of God with a song, and will magnify him with thanksgiving.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
[This] also shall please the LORD better than an ox [or] bullock that hath horns and hoofs.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
The humble shall see [this, and] be glad: and your heart shall live that seek God.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
For the LORD heareth the poor, and despiseth not his prisoners.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Let the heaven and earth praise him, the seas, and every thing that moveth therein.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
For God will save Zion, and will build the cities of Judah: that they may dwell there, and have it in possession.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
The seed also of his servants shall inherit it: and they that love his name shall dwell therein.

< Zabura 69 >