< Zabura 68 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
For the end, a Psalm of a Song by David. Let God arise, and let his enemies be scattered; and let them that hate him flee from before him.
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
As smoke vanishes, let them vanish: as wax melts before the fire, so let the sinners perish from before God.
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
But let the righteous rejoice; let them exult before God: let them be delighted with joy.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Sing to God, sing praises to his name: make a way for him that rides upon the west (the Lord is his name) and exult before him. They shall be troubled before the face of him,
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
[who is] the father of the orphans, and judge of the widows: [such is] God in his holy place.
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
God settles the solitary in a house; leading forth prisoners mightily, also them that act provokingly, [even] them that dwell in tombs.
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
O God, when thou wentest forth before thy people, when thou wentest through the wilderness; (Pause)
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
the earth quaked, yea, the heavens dropped [water] at the presence of the God of Sina, at the presence of the God of Israel.
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
O God, thou wilt grant to thine inheritance a gracious rain; for it was weary, but thou didst refresh it.
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Thy creatures dwell in it: thou hast in thy goodness prepared for the poor.
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
The Lord God will give a word to them that preach [it] in a great company.
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
The king of the forces of the beloved, of the beloved, [will] even [grant them] for the beauty of the house to divide the spoils.
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
Even if ye should lie among the lots, [ye shall have] the wings of a dove covered with silver, and her breast with yellow gold.
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
When the heavenly One scatters kings upon it, they shall be made snow-white in Selmon.
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
The mountain of God is a rich mountain; a swelling mountain, a rich mountain.
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
Wherefore do ye conceive [evil], ye swelling mountains? [this is] the mountain which God has delighted to dwell in; yea, the Lord will dwell [in it] for ever.
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
The chariots of God are ten thousand fold, thousands of rejoicing ones: the Lord is among them, in Sina, in the holy place.
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
Thou art gone up on high, thou hast led captivity captive, thou hast received gifts for man, yea, for [they were] rebellious, that thou mightest dwell among them.
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Blessed be the Lord God, blessed be the Lord daily; and the God of our salvation shall prosper us. (Pause)
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
Our God is the God of salvation; and to the Lord belong the issues from death.
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
But God shall crust the heads of his enemies; the hairy crown of them that go on in their trespasses.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
The Lord said, I will bring again from Basan, I will bring [my people] again through the depths of the sea.
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
That thy foot may be dipped in blood, [and] the tongue of thy dogs [be stained] with that of [thine] enemies.
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
Thy goings, O God, have been seen; the goings of my God, the king, in the sanctuary.
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
The princes went first, next before the players on instruments, in the midst of damsels playing on timbrels.
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
Praise God in the congregations, the Lord from the fountains of Israel.
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
There is Benjamin the younger [one] in ecstasy, the princes of Juda their rulers, the princes of Zabulon, the princes of Nephthali.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
O God, command thou thy strength: strengthen, O God, this which thou hast wrought in us.
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
Because of thy temple at Jerusalem shall kings bring presents to thee.
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
Rebuke the wild beasts of the reed: let the crowd of bulls with the heifers of the nations [be rebuked], so that they who have been proved with silver may not be shut out: scatter thou the nations that wish for wars.
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Ambassadors shall arrive out of Egypt; Ethiopia shall hasten [to stretch out] her hand readily to God.
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
Sing to God, ye kingdoms of the earth; sing psalms to the Lord. (Pause)
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
Sing to God that rides on the heaven of heaven, eastward: lo, he will utter a mighty sound with his voice.
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
Give ye glory to God: his excellency is over Israel, and his power is in the clouds.
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
God is wonderful in his holy [places], the God of Israel: he will give power and strength to his people: blessed be God.

< Zabura 68 >