< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
Načelniku godbe, psalm Davidov. Čuj, o Bog, glas moj, ko premišljujem; strahu sovražnikovega varuj življenje moje.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Skrivaj me skrivnemu naklepu hudobnih, ropotanju njih, ki delajo krivico:
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
Ki brusijo kakor meč jezik svoj, napenjajo kakor pušico svojo bridko besedo.
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
S kopjem napadajo poštenjaka iz zakotja; nenadoma ga napadajo s kopjem in se ne bojé.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
Potrjujejo si reč hudobno; o skrivanji zank govoré; pravijo: Kdo bi jih videl?
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Preiskujejo krivice; oslabeli smo po tem, kar so tako zvito preiskali; tako globoko je osrčje moža in srce.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
Ali ko jih bode Bog napadel s kopjem, pušica nagla bodejo njih udarci.
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
In storili bodejo, da sè samim jezikom svojim udarijo sebe; razkropljeni se bodejo spustili v beg, kdorkoli jih bode videl.
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
Katerikoli pa ljudjé se bojé, oznanjali bodo delo Božje in dejanje njegovo stavili pred óči.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Veselil se bode pravični v Gospodu, in pribežal k njemu; ponašali se bodo vsi, ki so pravega srca.

< Zabura 64 >