< Zabura 59 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
Osvobodi me pred mojimi sovražniki, oh moj Bog. Brani me pred tistimi, ki se dvigujejo zoper mene.
2 Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
Osvobodi me pred delavci krivičnosti in reši me pred krvoločnimi ljudmi.
3 Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
Kajti, glej, za mojo dušo prežijo v zasedi, mogočni so se zbrali zoper mene; ne zaradi mojega prestopka niti ne zaradi mojega greha, oh Gospod.
4 Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
Brez moje krivde tečejo in se pripravljajo. Zbudi se, da mi pomagaš in glej.
5 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
Ti torej, oh Gospod Bog nad bojevniki, Izraelov Bog, zbudi se, da obiščeš vse pogane. Z nobenim zlobnim prestopnikom ne bodi usmiljen. (Sela)
6 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
Vračajo se zvečer, zganjajo hrup kakor pes in krožijo po mestu.
7 Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
Glej, s svojimi usti bruhajo, meči so na njihovih ustnicah, kajti pravijo: »Kdo sliši?«
8 Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
Toda ti, oh Gospod, se jim boš posmehoval, vse pogane boš imel v posmeh.
9 Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
Zaradi njegove moči bom čakal nate, kajti Bog je moja obramba.
10 Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
Bog mojega usmiljenja me bo vodil. Bog mi bo dal videti mojo željo na mojih sovražnikih.
11 Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
Ne ubij jih, da ne bi moje ljudstvo pozabilo. Razkropi jih s svojo močjo in zlomi jih, oh Gospod, naš ščit.
12 Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
Zaradi greha njihovih ust in besed njihovih ustnic naj bodo celó prijeti v svojem ponosu in za preklinjanje in laži, katere govorijo.
13 ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
Použij jih v besu, použij jih, da jih ne bo in naj spoznajo, da Bog vlada v Jakobu do koncev zemlje. (Sela)
14 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
Zvečer naj se vrnejo in naj zganjajo hrup kakor pes ter krožijo po mestu.
15 Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
Naj se potikajo gor in dol za hrano in godrnjajo, če ne bodo nasičeni.
16 Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
Toda jaz bom prepeval o tvoji moči, da, zjutraj bom na glas prepeval o tvojem usmiljenju, kajti ti si bil moja obramba in zatočišče na dan moje stiske.
17 Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.
Tebi, oh moja moč, bom prepeval, kajti Bog je moja obramba in Bog mojega usmiljenja.

< Zabura 59 >