< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
Au maître de chant. Psaume des fils de Coré. Ecoutez tous ceci, ô peuples; prêtez l'oreille vous tous habitants du monde,
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
hommes du commun et hommes de condition, ensemble riches et pauvres.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
Ma bouche va faire entendre des paroles sages, et mon cœur a des pensées pleines de sens.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
Je prête l'oreille aux sentences que Dieu m'inspire; j'explique mon énigme au son de la harpe.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Pourquoi craindrais-je aux jours du malheur, lorsque l'iniquité de mes persécuteurs m'assiège?
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
Eux qui mettent leur confiance dans leurs biens, leur gloire dans leurs grandes richesses!
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
Un homme ne peut racheter son frère, ni payer à Dieu sa rançon.
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
Le rachat de leur vie est trop cher; il est à jamais impossible,
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
pour qu'il vive éternellement, et qu'il ne voie jamais la fosse.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Non, il la verra; les sages meurent, l'insensé et le stupide périssent également, laissant à d'autres leurs biens.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
Ils s'imaginent que leurs maisons seront éternelles, que leurs demeures subsisteront d'âge en âge, et ils donnent leurs noms à leurs domaines.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Mais, même dans sa splendeur, l'homme ne dure pas; il est semblable aux biches qui périssent.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
Tel est leur sort, à ces hommes si confiants, et à ceux qui les suivent en approuvant leurs discours. — Séla.
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
Comme un troupeau, ils sont poussés dans le schéol, la mort est leur pasteur; le matin, les hommes droits dominent sur eux, et leur ombre se consumera au schéol, sans autre demeure. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
Mais Dieu rachètera mon âme de la puissance du schéol, car il me prendra avec lui. — Séla. (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Ne crains donc pas, quand un homme s'enrichit, quand s'accroît l'opulence de sa maison.
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
Car il n'emportera rien à sa mort, son opulence ne descendra pas avec lui.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Il aura beau s'estimer heureux pendant sa vie; on aura beau te louer des jouissances que tu te donnes:
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
Tu iras rejoindre la génération de tes pères, qui jamais ne reverront la lumière.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
L'homme, même dans sa splendeur, ne comprend pas, il est semblable aux bêtes qui périssent.

< Zabura 49 >