< Zabura 45 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Lili.” Na’ya’yan Kora maza. Maskil Waƙar Aure. Zuciyata ta cika da kyakkyawan kan magana yayinda nake rera ayoyina wa sarki; harshena ne alƙalamin ƙwararren marubuci.
For the end, for alternate [strains] by the sons of Core; for instruction, a Song concerning the beloved. My heart has uttered a good matter: I declare my works to the king: my tongue is the pen of a quick writer.
2 Kai ne mafi kyau cikin mutane an kuma shafe leɓunanka da alheri, da yake Allah ya albarkace ka har abada.
Thou art more beautiful than the sons of men: grace has been shed forth on thy lips: therefore God has blessed thee for ever.
3 Ka ɗaura takobinka a gefenka, ya jarumi; ka rufe kanka da ɗaukaka da kuma daraja.
Gird thy sword upon thy thigh, O Mighty One, in thy comeliness, and in thy beauty;
4 Cikin darajarka ka hau zuwa nasara a madadin gaskiya, tawali’u da adalci; bari hannunka na dama yă nuna ayyukan banmamaki.
and bend [thy bow], and prosper, and reign, because of truth and meekness and righteousness; and thy right hand shall guide thee wonderfully.
5 Bari kibiyoyinka masu tsini su huda zukatan abokan gāban sarki; bari al’ummai su fāɗi ƙarƙashin ƙafafunka.
Thy weapons are sharpened, Mighty One, (the nations shall fall under thee) [they are] in the heart of the king's enemies.
6 Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin; sandar adalci zai zama sandar mulkinka.
Thy throne, O God, is for ever and ever: the sceptre of thy kingdom is a sceptre of righteousness.
7 Kana ƙaunar abin da yake daidai kana kuma ƙin mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya sa ka a bisa abokanka ta wurin shafe ka da man farin ciki.
Thou hast loved righteousness, and hated iniquity: therefore God, thy God, has anointed thee with the oil of gladness beyond thy fellows.
8 Dukan rigunanka suna ƙanshin turaren mur da na aloyes, da na kashiya; daga kowace fadan da aka yi masa ado da hauren giwa kaɗe-kaɗen tsirkiya kan sa ka murna.
Myrrh, and stacte, and cassia [are exhaled] from thy garments, [and] out of the ivory palaces,
9 ’Ya’yan sarki mata suna cikin matan da ake girmama; a hannun damarka kuwa ga amarya, sarauniya saye da ofir zinariya.
with which kings' daughters have gladdened thee for thine honour: the queen stood by on thy right hand, clothed in vesture wrought with gold, [and] arrayed in divers colours.
10 Ki saurara, ya ke diya, ki lura ku kuma kasa kunne, Ki manta da mutanenki da gidan mahaifinki.
Hear, O daughter, and see, and incline thine ear; forget also thy people, and thy father's house.
11 Sarki ya cika da sha’awar kyanki; ki girmama shi, gama shi ne maigidanki.
Because the king has desired thy beauty; for he is thy Lord.
12 Diyar Taya za tă zo da kyauta, mawadata za su nemi tagomashinki.
And the daughter of Tyre shall adore him with gifts; the rich of the people of the land shall supplicate thy favour.
13 Gimbiya tana fada, kyakkyawa ce ainun; an saƙa rigarta da zaren zinariya.
All her glory [is that] of the daughter of the king of Esebon, robed [as she is] in golden fringed garments,
14 Cikin riguna masu ado aka kai ta wurin sarki; abokanta budurwai suna biye da ita aka kuwa kawo su gare ka.
in embroidered [clothing]: virgins shall be brought to the king after her: her fellows shall be brought to thee.
15 Aka bi da su cikin farin ciki da murna; suka shiga fadan sarki.
They shall be brought with gladness and exultation: they shall be led into the king's temple.
16 ’Ya’yanka maza za su maye matsayin kakanninka; za ka sa su yi mulki a duk fāɗin ƙasar.
Instead of thy fathers children are born to thee: thou shalt make them princes over all the earth.
17 Zan sa a tuna da kai a dukan zamanai; saboda haka al’ummai za su yabe ka har abada abadin.
They shall make mention of thy name from generation to generation: therefore shall the nations give thanks to thee for ever, even for ever and ever.

< Zabura 45 >