< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
Untuk pemimpin kor. Mazmur Daud. Berbahagialah orang yang memperhatikan orang yang lemah; TUHAN akan menolong dia di waktu kesesakan.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
TUHAN akan melindungi dan memelihara dia, Ia akan membahagiakannya di bumi, dan tidak menyerahkan dia ke tangan musuhnya.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
TUHAN akan menolong dia pada waktu sakit, dan memulihkan kesehatannya.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
Kataku, "Aku telah berdosa terhadap-Mu, ya TUHAN, kasihanilah aku dan sembuhkanlah aku."
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
Musuhku mengatakan yang jahat tentang aku, mereka ingin agar aku mati dan dilupakan.
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
Orang-orang yang menjenguk aku tidak tulus ikhlas. Mereka mengumpulkan kabar buruk tentang aku, lalu menyiarkannya ke mana-mana.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
Semua yang membenci aku berbisik-bisik; mereka mengatakan yang paling jelek tentang aku.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
Kata mereka, "Penyakitnya parah sekali, ia tak mungkin bangun lagi."
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Bahkan kawan karib yang paling kupercayai, orang yang makan bersamaku, telah menghina aku.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
Kasihanilah aku ya TUHAN, sembuhkanlah aku, agar aku dapat membalas kejahatan lawan-lawanku.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
Kalau aku tidak dikalahkan musuhku, tahulah aku bahwa Engkau berkenan kepadaku.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
Engkau menolong aku karena ketulusanku, dan membuat aku hidup bersama-Mu untuk selamanya.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
Pujilah TUHAN, Allah Israel! Pujilah Dia sekarang dan selama-lamanya! Jadilah demikian. Amin!

< Zabura 41 >