< Zabura 41 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
To the chief music-maker. A Psalm. Of David. Happy is the man who gives thought to the poor; the Lord will be his saviour in the time of trouble.
2 Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
The Lord will keep him safe, and give him life; the Lord will let him be a blessing on the earth, and will not give him into the hand of his haters.
3 Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
The Lord will be his support on his bed of pain: by you will all his grief be turned to strength.
4 Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
I said, Lord, have mercy on me; make my soul well, because my faith is in you.
5 Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
My haters say evil against me, When will he be dead, and his name come to an end?
6 Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
If one comes to see me, deceit is in his heart; he keeps a store of evil, which he makes public in every place.
7 Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
All my haters are talking secretly together against me; they are designing my downfall.
8 “Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
They say, He has an evil disease, which will not let him go: and now that he is down he will not get up again.
9 Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Even my dearest friend, in whom I had faith, who took bread with me, is turned against me.
10 Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
But you, O Lord, have mercy on me, lifting me up, so that I may give them their punishment.
11 Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
By this I see that you have pleasure in me, because my hater does not overcome me.
12 Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
And as for me, you are my support in my righteousness, giving me a place before your face for ever.
13 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.
May the Lord God of Israel be praised, through eternal days and for ever. So be it. So be it.

< Zabura 41 >