< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
Ein Psalm Davids, da er seine Gebärde verstellte vor Abimelech, als der ihn von sich trieb und er wegging. Ich will den HERRN loben allezeit; sein Lob soll immerdar in meinem Munde sein.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
Meine Seele soll sich rühmen des HERRN, daß es die Elenden hören und sich freuen.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Preiset mit mir den HERRN und laßt uns miteinander seinen Namen erhöhen.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
Da ich den HERRN suchte, antwortete er mir und errettete mich aus aller meiner Furcht.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Welche auf ihn sehen, die werden erquickt, und ihr Angesicht wird nicht zu Schanden.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
Da dieser Elende rief, hörte der HERR und half ihm aus allen seinen Nöten.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
Der Engel des HERRN lagert sich um die her, so ihn fürchten, und hilft ihnen aus.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Schmecket und sehet, wie freundlich der HERR ist. Wohl dem, der auf ihn traut!
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Fürchtet den HERRN, ihr seine Heiligen! denn die ihn fürchten, haben keinen Mangel.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Reiche müssen darben und hungern; aber die den HERRN suchen, haben keinen Mangel an irgend einem Gut.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Kommt her, Kinder, höret mir zu; ich will euch die Furcht des HERRN lehren:
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Wer ist, der Leben begehrt und gerne gute Tage hätte?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Behüte deine Zunge vor Bösem und deine Lippen, daß sie nicht Trug reden.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Laß vom Bösen und tue Gutes; suche Frieden und jage ihm nach.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Die Augen des HERRN merken auf die Gerechten und seine Ohren auf ihr Schreien;
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
das Antlitz aber des HERRN steht gegen die, so Böses tun, daß er ihr Gedächtnis ausrotte von der Erde.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
Wenn die Gerechten schreien, so hört der HERR und errettet sie aus all ihrer Not.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Der HERR ist nahe bei denen, die zerbrochnes Herzens sind, und hilft denen, die ein zerschlagen Gemüt haben.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Der Gerechte muß viel Leiden; aber der HERR hilft ihm aus dem allem.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
Er bewahrt ihm alle seine Gebeine, daß deren nicht eins zerbrochen wird.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Den Gottlosen wird das Unglück töten; und die den Gerechten hassen, werden Schuld haben.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Der HERR erlöst die Seele seiner Knechte; und alle, die auf ihn trauen, werden keine Schuld haben.

< Zabura 34 >