< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Shout for joy in the Lord, you righteous: praise for the upright is seemly.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Give thanks to the Lord on the lyre, play to him on a ten-stringed harp.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Sing to him a new song, play skilfully and shout merrily.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
For the Lord is straight in his promise; and all that he does is in faithfulness.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Justice and right he loves; the earth is full of his kindness.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
By his word the heavens were made, all their host by the breath of his mouth.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
He gathers the sea in a bottle, the ocean he puts into store-houses.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Let the whole world honour the Lord, let all who live on earth be in awe.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
For at his word it came into being, at his command it stood forth.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
The Lord frustrates the designs of the nations, what the peoples have purposed, he brings to nought,
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
but the Lord’s own design will stand forever, and what his heart has purposed, through all generations.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Happy the nation whose God is the Lord, the people he chose for himself as his own.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
The Lord looks down from heaven, he sees all of humanity;
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
from where he rules he gazes on all who inhabit the earth.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
He fashions the hearts of them all, and gives heed to all that they do.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
It is not by great armies that kings are victorious, it is not by great strength that a warrior saves himself;
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
false hope is the war-horse to usher in victory, for all its great might it can provide no escape.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
See! The eye of the Lord is on those who fear him, on those who hope in his kindness;
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
to deliver their life from death, and to keep them alive in famine.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
We wait for the Lord: he is our help and our shield.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
For in him our heart is glad, we trust in his holy name.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Let your kindness, O Lord, be upon us, as is our hope in you.

< Zabura 33 >