< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
For the leader; set to “Deer of the Dawn”. A psalm of David. My God, my God, why have you left me, my rescue so far from the words of my roaring?
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
I cry in the day, you do not answer, I cry in the night but find no rest.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
You are the Holy One, throned on the praises of Israel.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
In you our ancestors trusted, they trusted and you delivered them.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
They cried to you, and found safety, in you did they trust and were not put to shame.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
But I am a worm, not a person; insulted by others, despised by the people.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
All who see me mock me, with mouths wide open and wagging heads:
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
‘He relies on the Lord; let him save him. Let him rescue the one he holds dear!’
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
But you drew me from the womb, laid me safely on my mother’s breasts.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
On your care was I cast from my very birth, you are my God from my mother’s womb.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Be not far from me, for trouble is nigh, and there is none to help.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
I am circled by many bulls, beset by the mighty of Bashan,
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
who face me with gaping jaws, like ravening roaring lions.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Poured out am I like water, and all my bones are loosened. My heart is become like wax, melted within me.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
My palate is dry as a sherd, my tongue sticks to my jaws; in the dust of death you lay me.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
For dogs are round about me, a band of knaves encircles me, gnawing my hands and my feet.
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
I can count my bones, every one. As for them, they feast their eyes on me.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
They divide my garments among them, and over my raiment cast lots.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
But you, O Lord, be not far, O my strength, hasten to help me.
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Deliver my life from the sword my life from the power of the dogs.
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Save me from the jaws of the lion, from the horns of the wild oxen help me.
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
I will tell of your fame to my kindred, and in the assembly will praise you.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
Praise the Lord, you who fear him. All Jacob’s seed, give him glory. All Israel’s seed, stand in awe of him.
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
For he has not despised nor abhorred the sorrow of the sorrowful. He hid not his face from me, but he listened to my cry for help.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Of you is my praise in the great congregation; my vows I will pay before those who fear him.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
The afflicted will eat to their heart’s desire, and those who seek after the Lord will praise him. Lift up your hearts forever.
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
All will call it to mind, to the ends of the earth, and turn to the Lord; and all tribes of the nations will bow down before you.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
For the kingdom belongs to the Lord: he is the Lord of the nations.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
To him will bow down all who sleep in the earth, and before him bend all who go down to the dust, and those who could not preserve their lives.
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
My descendants will tell of the Lord to the next generation;
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
they will declare his righteousness to people yet to be born: He has done it.

< Zabura 22 >