< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
大卫的诗,交与伶长。调用朝鹿。 我的 神,我的 神!为什么离弃我? 为什么远离不救我?不听我唉哼的言语?
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
我的 神啊,我白日呼求,你不应允, 夜间呼求,并不住声。
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
但你是圣洁的, 是用以色列的赞美为宝座的。
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
我们的祖宗倚靠你; 他们倚靠你,你便解救他们。
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
他们哀求你,便蒙解救; 他们倚靠你,就不羞愧。
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
但我是虫,不是人, 被众人羞辱,被百姓藐视。
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
凡看见我的都嗤笑我; 他们撇嘴摇头,说:
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
他把自己交托耶和华,耶和华可以救他吧! 耶和华既喜悦他,可以搭救他吧!
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
但你是叫我出母腹的; 我在母怀里,你就使我有倚靠的心。
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
我自出母胎就被交在你手里; 从我母亲生我,你就是我的 神。
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
求你不要远离我! 因为急难临近了,没有人帮助我。
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
有许多公牛围绕我, 巴珊大力的公牛四面困住我。
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
它们向我张口, 好像抓撕吼叫的狮子。
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
我如水被倒出来; 我的骨头都脱了节; 我心在我里面如蜡熔化。
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
我的精力枯干,如同瓦片; 我的舌头贴在我牙床上。 你将我安置在死地的尘土中。
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
犬类围着我,恶党环绕我; 他们扎了我的手,我的脚。
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
我的骨头,我都能数过; 他们瞪着眼看我。
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
他们分我的外衣, 为我的里衣拈阄。
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
耶和华啊,求你不要远离我! 我的救主啊,求你快来帮助我!
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
求你救我的灵魂脱离刀剑, 救我的生命脱离犬类,
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
救我脱离狮子的口; 你已经应允我,使我脱离野牛的角。
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
我要将你的名传与我的弟兄, 在会中我要赞美你。
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
你们敬畏耶和华的人要赞美他! 雅各的后裔都要荣耀他! 以色列的后裔都要惧怕他!
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
因为他没有藐视憎恶受苦的人, 也没有向他掩面; 那受苦之人呼吁的时候,他就垂听。
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
我在大会中赞美你的话是从你而来的; 我要在敬畏耶和华的人面前还我的愿。
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
谦卑的人必吃得饱足; 寻求耶和华的人必赞美他。 愿你们的心永远活着!
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
地的四极都要想念耶和华,并且归顺他; 列国的万族都要在你面前敬拜。
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
因为国权是耶和华的; 他是管理万国的。
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
地上一切丰肥的人必吃喝而敬拜; 凡下到尘土中—不能存活自己性命的人 —都要在他面前下拜。
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
他必有后裔事奉他; 主所行的事必传与后代。
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
他们必来把他的公义传给将要生的民, 言明这事是他所行的。

< Zabura 22 >