< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Para o regente. Do servo do SENHOR, chamado Davi, o qual falou as palavras deste cântico ao SENHOR, no dia em que o SENHOR o livrou das mãos de todos os seus inimigos, e das mãos de Saul. Ele disse: Eu te amarei, SENHOR, [tu és] minha força.
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
O SENHOR é minha rocha, e minha fortaleza, e meu libertador, meu Deus, meu rochedo, em quem confio; [é] meu escudo, e a força da minha salvação, meu alto refúgio.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Eu clamei ao SENHOR digno de louvor; e fiquei livre de meus inimigos.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Cordas de morte me cercaram; e riachos de maldade me encheram de medo.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
Cordas do Xeol me envolveram; laços de morte me afrontaram. (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
Em minha angústia, clamei ao SENHOR, e roguei a meu Deus; desde o seu Templo ele ouviu a minha voz; e o meu clamor diante de seu rosto chegou aos ouvidos dele.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Então a terra de abalou e tremeu; e os fundamentos dos montes de moveram e foram abalados, porque ele se irritou.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Fumaça subiu de seu nariz, e fogo consumidor saiu de sua boca; carvões foram acesos por ele.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Ele moveu os céus, e desceu; e as trevas [estavam] debaixo de seus pés.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Ele montou sobre um querubim, e fez seu voo; e voou veloz sobre as assas do vento.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Ele pôs as trevas como seu esconderijo; pôs a sua tenda ao redor dele; trevas das águas, nuvens dos céus.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Do brilho de sua presença suas nuvens se espalharam, [e também] a saraiva, e as brasas de fogo.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
E o SENHOR trovejou nos céus; e o Altíssimo soltou sua voz; saraiva e brasas de fogo [caíram].
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Ele mandou suas flechas, e os dispersou; e [lançou] muitos raios, e os perturbou.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
E as profundezas das águas foram vistas, e os fundamentos do mundo foram descobertos por tua repreensão, SENHOR, pelo sopro do vento do teu nariz.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Desde o alto ele enviou, [e] me tomou; tirou-me de muitas águas.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Ele me livrou do meu forte inimigo, e daqueles que me odeiam; porque eles eram mais poderosos do que eu.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Eles me confrontaram no dia de minha calamidade; mas o SENHOR ficou junto de mim.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Ele me tirou para um lugar amplo; ele me libertou, porque se agradou de mim.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
O SENHOR me recompensou conforme a minha justiça; conforme a pureza das minhas mãos ele me retribuiu.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Porque eu guardei os caminhos do SENHOR; nem me [afastei] do meu Deus praticando o mal.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Porque todos os juízos dele estavam diante de mim; e não rejeitei seus estatutos para mim.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
Mas eu fui fiel com ele; e tomei cuidado contra minha maldade.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Assim o SENHOR me recompensou conforme a minha justiça; conforme a pureza de minhas mãos perante seus olhos.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Com o bondoso tu te mostras bondoso; [e] com o homem fiel tu te mostras fiel.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
Com o puro tu te mostras puro; mas com o perverso tu te mostras agressivo.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Porque tu livras ao povo aflito, e humilhas aos olhos que se exaltam.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Porque tu acendes minha lâmpada; o SENHOR meu Deus ilumina as minhas trevas.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Porque contigo eu marcho [contra] um exército; e com meu Deus eu salto um muro.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
O caminho de Deus é perfeito; a palavra do SENHOR é refinada; ele [é] escudo para todos os que nele confiam.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Porque quem é Deus, a não ser o SENHOR? E quem é rocha, a não ser o nosso Deus?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Deus [é] o que me veste de força; e o que dá perfeição ao meu caminho.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Ele faz meus pés como o das cervas; e me põe em meus lugares altos.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Ele ensina minhas mãos para a guerra, [de modo que] um arco de bronze se quebra em meus braços.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Também tu me deste o escudo de tua salvação, e tua mão direita me sustentou; e tua mansidão me engrandeceu.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Tu alargaste os meus passos abaixo de mim; e meus pés não vacilaram.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Persegui a meus inimigos, e eu os alcancei; e não voltei até os exterminá-los.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Eu os perfurei, que não puderam mais se levantar; caíram debaixo dos meus pés.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Porque tu me preparaste com força para a batalha; fizeste se curvarem abaixo de mim aqueles que contra mim tinham se levantado.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
E tu me deste a nuca de meus inimigos; destruí aos que me odiavam.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Eles clamaram, mas não havia quem os livrasse; [clamaram até] ao SENHOR, mas ele não lhes respondeu.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Então eu os reduzi a pó, como a poeira ao vento; eu os joguei fora como a lama das ruas.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Tu me livraste das brigas do povo; tu me puseste como cabeça das nações; o povo que eu não conhecia me serviu.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Ao [me] ouvirem, [logo] me obedeceram; estrangeiros se sujeitaram a mim.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Estrangeiros se enfraqueceram; e tremeram de medo desde suas extremidades.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
O SENHOR vive, e bendito [seja] minha rocha; e exaltado [seja] o Deus de minha salvação;
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
O Deus que dá minha vingança, e sujeita aos povos debaixo de mim;
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Aquele que me livra dos meus inimigos; tu também me exaltas sobre aqueles que se levantam contra mim; tu me livras do homem violento.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Por isso, SENHOR, eu te louvarei entre as nações, e cantarei ao teu Nome;
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Que faz grandes as salvações de seu Rei, e pratica a bondade para com o seu ungido, com Davi, e sua semente, para sempre.

< Zabura 18 >