< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
In finem, puero Domini David, qui locutus est Domino verba cantici huius, in die, qua eripuit eum Dominus de manu omnium inimicorum eius, et de manu Saul, et dixit: Diligam te Domine fortitudo mea:
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Dominus firmamentum meum, et refugium meum, et liberator meus. Deus meus adiutor meus, et sperabo in eum. Protector meus, et cornu salutis meæ, et susceptor meus.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Laudans invocabo Dominum: et ab inimicis meis salvus ero.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Circumdederunt me dolores mortis: et torrentes iniquitatis conturbaverunt me.
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
Dolores inferni circumdederunt me: præoccupaverunt me laquei mortis. (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
In tribulatione mea invocavi Dominum, et ad Deum meum clamavi: et exaudivit de templo sancto suo vocem meam: et clamor meus in conspectu eius, introivit in aures eius.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Commota est, et contremuit terra: fundamenta montium conturbata sunt, et commota sunt, quoniam iratus est eis.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Ascendit fumus in ira eius: et ignis a facie eius exarsit: carbones succensi sunt ab eo.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Inclinavit cælos, et descendit: et caligo sub pedibus eius.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Et ascendit super cherubim, et volavit: volavit super pennas ventorum.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Et posuit tenebras latibulum suum, in circuitu eius tabernaculum eius: tenebrosa aqua in nubibus aeris.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Præ fulgore in conspectu eius nubes transierunt, grando et carbones ignis.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Et intonuit de cælo Dominus, et Altissimus dedit vocem suam: grando et carbones ignis.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Et misit sagittas suas, et dissipavit eos: fulgura multiplicavit, et conturbavit eos.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Et apparuerunt fontes aquarum, et revelata sunt fundamenta orbis terrarum: Ab increpatione tua Domine, ab inspiratione Spiritus iræ tuæ.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Misit de summo, et accepit me: et assumpsit me de aquis multis.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Eripuit me de inimicis meis fortissimis, et ab his qui oderunt me: quoniam confortati sunt super me.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Prævenerunt me in die afflictionis meæ: et factus est Dominus protector meus.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Et eduxit me in latitudinem: salvum me fecit, quoniam voluit me.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Et retribuet mihi Dominus secundum iustitiam meam, et secundum puritatem manuum mearum retribuet mihi:
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Quia custodivi vias Domini, nec impie gessi a Deo meo.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Quoniam omnia iudicia eius in conspectu meo: et iustitias eius non repuli a me.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
Et ero immaculatus cum eo: et observabo me ab iniquitate mea.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Et retribuet mihi Dominus secundum iustitiam meam: et secundum puritatem manuum mearum in conspectu oculorum eius.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Cum sancto sanctus eris, et cum viro innocente innocens eris:
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
et cum electo electus eris: et cum perverso perverteris.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Quoniam tu populum humilem salvum facies: et oculos superborum humiliabis.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Quoniam tu illuminas lucernam meam Domine: Deus meus illumina tenebras meas.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Quoniam in te eripiar a tentatione, et in Deo meo transgrediar murum.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Deus meus impolluta via eius: eloquia Domini igne examinata: protector est omnium sperantium in se.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Quoniam quis Deus præter Dominum? aut quis Deus præter Deum nostrum?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Deus qui præcinxit me virtute: et posuit immaculatam viam meam.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Qui perfecit pedes meos tamquam cervorum, et super excelsa statuens me.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Qui docet manus meas ad prælium: et posuisti, ut arcum æreum, brachia mea.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Et dedisti mihi protectionem salutis tuæ: et dextera tua suscepit me: Et disciplina tua correxit me in finem: et disciplina tua ipsa me docebit.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Dilatasti gressus meos subtus me: et non sunt infirmata vestigia mea:
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Persequar inimicos meos, et comprehendam illos: et non convertar donec deficiant.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Confringam illos, nec poterunt stare: cadent subtus pedes meos.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Et præcinxisti me virtute ad bellum: et supplantasti insurgentes in me subtus me.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Et inimicos meos dedisti mihi dorsum, et odientes me disperdidisti.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Clamaverunt, nec erat qui salvos faceret, ad Dominum: nec exaudivit eos.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Et comminuam eos, ut pulverem ante faciem venti: ut lutum platearum delebo eos.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Eripies me de contradictionibus populi: constitues me in caput Gentium.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Populus, quem non cognovi, servivit mihi: in auditu auris obedivit mihi.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Filii alieni mentiti sunt mihi, filii alieni inveterati sunt, et claudicaverunt a semitis suis.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Vivit Dominus, et benedictus Deus meus, et exaltetur Deus salutis meæ.
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
Deus qui das vindictas mihi, et subdis populos sub me, liberator meus de inimicis meis iracundis.
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Et ab insurgentibus in me exaltabis me: a viro iniquo eripies me.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Propterea confitebor tibi in nationibus Domine: et nomini tuo psalmum dicam,
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
magnificans salutes regis eius, et faciens misericordiam christo suo David, et semini eius usque in sæculum.

< Zabura 18 >