< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Il dit donc: Je t'aimerai, ô Éternel, qui es ma force!
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Éternel, mon rocher, ma forteresse et mon libérateur! Mon Dieu, mon rocher où je me réfugie! Mon bouclier, la force qui me délivre, ma haute retraite!
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Je m'écrie: Loué soit l'Éternel! et je suis délivré de mes ennemis.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Les liens de la mort m'avaient enveloppé, et les torrents de la destruction m'avaient épouvanté;
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
Les liens du Sépulcre m'entouraient, les pièges de la mort m'avaient surpris; (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
Dans ma détresse, j'invoquai l'Éternel, et je criai à mon Dieu. De son palais, il entendit ma voix, et les cris que je poussais vers lui parvinrent à ses oreilles.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Alors la terre fut ébranlée et trembla; les fondements des montagnes s'agitèrent et s'ébranlèrent, parce qu'il était courroucé.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Une fumée montait de ses narines, et de sa bouche un feu dévorant; il en jaillissait des charbons embrasés.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Il abaissa les cieux et descendit, ayant l'obscurité sous ses pieds.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Il était monté sur un chérubin, et il volait; il était porté sur les ailes du vent.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Il fit des ténèbres sa retraite; il mit autour de lui, comme une tente, des eaux ténébreuses, de noirs nuages.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
De la splendeur qui était devant lui, s'échappaient des nuées, avec de la grêle et des charbons de feu.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Et l'Éternel tonna dans les cieux, le Très-Haut fit retentir sa voix, avec de la grêle et des charbons de feu.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Il lança ses flèches, et dispersa mes ennemis; il lança des éclairs nombreux, et les mit en déroute.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Alors le fond des eaux apparut, et les fondements du monde furent mis à découvert, au bruit de ta menace, ô Éternel, au souffle du vent de ta colère.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Il étendit sa main d'en haut, et me prit; il me tira des grosses eaux.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Il me délivra de mon ennemi puissant, et de mes adversaires qui étaient plus forts que moi.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Ils m'avaient surpris au jour de ma calamité; mais l'Éternel fut mon appui.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Il m'a mis au large, il m'a délivré, parce qu'il a pris son plaisir en moi.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
L'Éternel m'a traité selon ma justice; il m'a rendu selon la pureté de mes mains.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Car j'ai gardé les voies de l'Éternel, et je n'ai point été infidèle à mon Dieu.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Car toutes ses ordonnances sont devant moi, et je ne m'écarte point de ses statuts.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
J'ai été intègre avec lui, et je me suis gardé de mon péché.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Aussi l'Éternel m'a rendu selon ma justice, selon la pureté de mes mains devant ses yeux.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Avec celui qui est bon, tu es bon; avec l'homme intègre, tu es intègre.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
Avec celui qui est pur, tu te montres pur; mais avec le pervers, tu agis selon sa perversité.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Car c'est toi qui sauves le peuple affligé, et qui abaisses les yeux des superbes.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
C'est toi qui fais luire ma lampe; c'est l'Éternel mon Dieu qui éclaire mes ténèbres.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Car avec toi je fonds sur une troupe; avec mon Dieu je franchis la muraille.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
La voie de Dieu est parfaite; la parole de l'Éternel est éprouvée; il est un bouclier pour tous ceux qui se retirent vers lui.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Car qui est Dieu, sinon l'Éternel? Et qui est un rocher, sinon notre Dieu?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Le Dieu qui me ceint de force, et qui a rendu mon chemin sûr;
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Qui rend mes pieds semblables à ceux des biches, et me fait tenir sur mes hauteurs;
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Qui forme mes mains au combat, et mes bras bandent un arc d'airain.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Tu m'as donné le bouclier de ton salut; ta droite me soutient, et ta bonté me rend puissant.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Tu élargis le chemin sous mes pas, et mes talons ne chancellent point.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Je poursuis mes ennemis; je les atteins, et je ne reviens qu'après les avoir exterminés.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Je les frappe, et ils ne peuvent se relever; ils tombent sous mes pieds.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Car tu m'as ceint de force pour le combat, tu fais plier sous moi mes adversaires.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Tu fais tourner le dos à mes ennemis devant moi; ceux qui me haïssaient, je les détruis.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Ils crient, mais il n'y a point de libérateur; ils crient à l'Éternel, mais il ne leur répond pas.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Je les broie comme la poussière livrée au vent, je les jette au loin comme la boue des rues.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Tu me sauves des dissensions du peuple; tu me mets à la tête des nations; le peuple que je ne connaissais pas m'est assujetti.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Au bruit de mon nom, ils m'obéissent; les fils de l'étranger viennent me flatter.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Les fils de l'étranger défaillent, et sortent tremblants de leur retraite.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
L'Éternel est vivant! Et béni soit mon rocher! Que le Dieu de mon salut soit exalté,
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
Le Dieu qui me donne la vengeance, et qui range les peuples sous moi!
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Toi qui me délivres de mes ennemis, qui m'élèves au-dessus de mes adversaires, qui me délivres de l'homme violent!
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
C'est pourquoi je te louerai, ô Éternel, parmi les nations, et je chanterai à ton nom.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
C'est lui qui délivre magnifiquement son roi, qui fait miséricorde à son Oint, à David et à sa postérité à jamais.

< Zabura 18 >