< Zabura 18 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Au chef de musique. Du serviteur de l’Éternel, de David, qui adressa à l’Éternel les paroles de ce cantique, le jour où l’Éternel l’eut délivré de la main de tous ses ennemis, et de la main de Saül. Et il dit: Je t’aimerai, ô Éternel, ma force!
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Éternel, mon rocher, et mon lieu fort, et celui qui me délivre! Mon Dieu, mon rocher, en qui je me confie, mon bouclier et la corne de mon salut, ma haute retraite!
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Je crierai à l’Éternel, qui est digne d’être loué, et je serai sauvé de mes ennemis.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Les cordeaux de la mort m’ont environné, et les torrents de Bélial m’ont fait peur;
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
Les cordeaux du shéol m’ont entouré, les filets de la mort m’ont surpris: (Sheol h7585)
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
Dans ma détresse j’ai invoqué l’Éternel, et j’ai crié à mon Dieu: de son temple, il a entendu ma voix, et mon cri est parvenu devant lui à ses oreilles.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Alors la terre fut ébranlée, et trembla, et les fondements des montagnes furent secoués et furent ébranlés, parce qu’il était irrité.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Une fumée montait de ses narines, et un feu sortant de sa bouche dévorait; des charbons en jaillissaient embrasés.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Et il abaissa les cieux, et descendit; et il y avait une obscurité profonde sous ses pieds.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Il était monté sur un chérubin, et volait, et il planait sur les ailes du vent.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Il mit les ténèbres pour sa demeure secrète comme sa tente autour de lui, des ténèbres d’eaux, d’épaisses nuées de l’air.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
De la splendeur qui était devant lui, ses nuées épaisses passaient, de la grêle et des charbons de feu.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Et l’Éternel tonna dans les cieux, et le Très-haut fit retentir sa voix, – de la grêle et des charbons de feu.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Et il tira ses flèches et dispersa [mes ennemis]; il lança des éclairs et les mit en déroute.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Alors les lits des eaux parurent, et les fondements du monde furent mis à découvert, quand tu les tanças, ô Éternel, par le souffle du vent de tes narines.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
D’en haut il étendit [sa main], il me prit, il me tira des grandes eaux;
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Il me délivra de mon puissant ennemi et de ceux qui me haïssaient; car ils étaient plus forts que moi.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Ils m’avaient surpris au jour de ma calamité, mais l’Éternel fut mon appui.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Et il me fit sortir au large, il me délivra, parce qu’il prenait son plaisir en moi.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
L’Éternel m’a récompensé selon ma justice, il m’a rendu selon la pureté de mes mains;
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Car j’ai gardé les voies de l’Éternel, et je ne me suis point méchamment détourné de mon Dieu.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Car toutes ses ordonnances ont été devant moi; et ses statuts, je ne les ai pas écartés de moi.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
Et j’ai été parfait avec lui, et je me suis gardé de mon iniquité.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Et l’Éternel m’a rendu selon ma justice, selon la pureté de mes mains devant ses yeux.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Avec celui qui use de grâce, tu uses de grâce; avec l’homme parfait, tu te montres parfait;
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
Avec celui qui est pur, tu te montres pur; et avec le pervers, tu es roide.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Car toi tu sauveras le peuple affligé, et tu abaisseras les yeux hautains.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Car c’est toi qui fais luire ma lampe: l’Éternel, mon Dieu, fait resplendir mes ténèbres.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Car, par toi, je courrai au travers d’une troupe, et, par mon Dieu, je franchirai une muraille.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Quant à Dieu, sa voie est parfaite; la parole de l’Éternel est affinée; il est un bouclier à tous ceux qui se confient en lui.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Car qui est Dieu, hormis l’Éternel, et qui est un rocher, si ce n’est notre Dieu,
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Le Dieu qui me ceint de force et qui rend ma voie parfaite? –
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Qui rend mes pieds pareils à ceux des biches, et me fait tenir debout sur mes lieux élevés;
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Qui enseigne mes mains à combattre, et mes bras bandent un arc d’airain.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Et tu m’as donné le bouclier de ton salut, et ta droite m’a soutenu, et ta débonnaireté m’a agrandi.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Tu as mis au large mes pas sous moi, et les chevilles de mes pieds n’ont pas chancelé.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
J’ai poursuivi mes ennemis, et je les ai atteints; et je ne m’en suis pas retourné que je ne les aie consumés.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Je les ai transpercés, et ils n’ont pu se relever; ils sont tombés sous mes pieds.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Et tu m’as ceint de force pour le combat; tu as courbé sous moi ceux qui s’élevaient contre moi.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Et tu as fait que mes ennemis m’ont tourné le dos; et ceux qui me haïssaient, je les ai détruits.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Ils criaient, et il n’y avait point de sauveur; [ils criaient] à l’Éternel, et il ne leur a pas répondu.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Et je les ai brisés menu comme la poussière devant le vent; je les ai jetés loin comme la boue des rues.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Tu m’as délivré des débats du peuple; tu m’as établi chef des nations; un peuple que je ne connaissais pas me servira.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Dès qu’ils ont entendu de leur oreille, ils m’ont obéi; les fils de l’étranger se sont soumis à moi en dissimulant.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Les fils de l’étranger ont dépéri, et ils sont sortis en tremblant de leurs lieux cachés.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
L’Éternel est vivant; et que mon Rocher soit béni! Et que le Dieu de mon salut soit exalté,
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
Le Dieu qui m’a donné des vengeances, et qui m’a assujetti les peuples,
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Qui m’a délivré de mes ennemis! Même tu m’as élevé au-dessus de ceux qui s’élèvent contre moi, tu m’as délivré de l’homme violent.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
C’est pourquoi, Éternel! je te célébrerai parmi les nations, et je chanterai des cantiques à [la gloire de] ton nom.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
[C’est lui] qui a donné de grandes délivrances à son roi, et qui use de bonté envers son oint, envers David, et envers sa semence, à toujours.

< Zabura 18 >