< Zabura 149 >

1 Yabi Ubangiji. Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, yabonsa a cikin taron tsarkaka.
Praise ye the Lord. Sing ye vnto the Lord a newe song: let his prayse be heard in the Congregation of Saints.
2 Bari Isra’ila su yi farin ciki da Mahaliccinsu; bari mutanen Sihiyona su yi murna da Sarkinsu.
Let Israel reioyce in him that made him, and let ye children of Zion reioyce in their King.
3 Bari su yabi sunansa tare da rawa suna kuma yin kiɗi gare shi da ganga da garaya.
Let them prayse his Name with the flute: let them sing prayses vnto him with the timbrell and harpe.
4 Gama Ubangiji yana jin daɗin mutanensa; yakan darjanta masu sauƙinkai da ceto.
For the Lord hath pleasure in his people: he will make the meeke glorious by deliuerance.
5 Bari tsarkaka su yi farin ciki a wannan bangirma su kuma rera don farin ciki a kan gadajensu.
Let ye Saints be ioyfull with glorie: let them sing loud vpon their beddes.
6 Bari yabon Allah yă kasance a bakunansu takobi mai kaifi kuma a hannuwansu,
Let the high Actes of God bee in their mouth, and a two edged sword in their hands,
7 don su ɗau fansa a kan al’ummai da kuma hukunci a kan mutane,
To execute vengeance vpon the heathen, and corrections among the people:
8 don su ɗaura sarakuna da sarƙoƙi, manyan garinsu da sarƙoƙin ƙarfe,
To binde their Kings in chaines, and their nobles with fetters of yron,
9 don su yi hukuncin da aka rubuta a kansu. Wannan ne ɗaukakar dukan tsarkakansa. Yabi Ubangiji.
That they may execute vpon them the iudgement that is written: this honour shall be to all his Saintes. Prayse ye the Lord.

< Zabura 149 >