< Zabura 147 >

1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Alleluya. Herie ye the Lord, for the salm is good; heriyng be myrie, and fair to oure God.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
The Lord schal bilde Jerusalem; and schal gadere togidere the scateryngis of Israel.
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Which Lord makith hool men contrit in herte; and byndith togidere the sorewes of hem.
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Which noumbrith the multitude of sterris; and clepith names to alle tho.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Oure Lord is greet, and his vertu is greet; and of his wisdom is no noumbre.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
The Lord takith vp mylde men; forsothe he makith low synneris `til to the erthe.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Bifore synge ye to the Lord in knoulechyng; seye ye salm to oure God in an harpe.
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Which hilith heuene with cloudis; and makith redi reyn to the erthe. Which bryngith forth hei in hillis; and eerbe to the seruice of men.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Which yyueth mete to her werk beestis; and to the briddys of crowis clepinge hym.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
He schal not haue wille in the strengthe of an hors; nether it schal be wel plesaunt to hym in the leggis of a man.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
It is wel plesaunt to the Lord on men that dreden hym; and in hem that hopen on his mercy.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Jerusalem, herie thou the Lord; Syon, herie thou thi God.
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
For he hath coumfortid the lockis of thi yatis; he hath blessid thi sones in thee.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
Which hath set thi coostis pees; and fillith thee with the fatnesse of wheete.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
Which sendith out his speche to the erthe; his word renneth swiftli.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Which yyueth snow as wolle; spredith abrood a cloude as aische.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
He sendith his cristal as mussels; who schal suffre bifore the face of his cooldnesse?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
He schal sende out his word, and schal melte tho; his spirit schal blowe, and watris schulen flowe.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Which tellith his word to Jacob; and hise riytfulnessis and domes to Israel.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
He dide not so to ech nacioun; and he schewide not hise domes to hem.

< Zabura 147 >