< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
In finem, Psalmus David. Domine probasti me, et cognovisti me:
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
tu cognovisti sessionem meam, et resurrectionem meam.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Intellexisti cogitationes meas de longe: semitam meam, et funiculum meum investigasti.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
Et omnes vias meas prævidisti: quia non est sermo in lingua mea.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Ecce Domine tu cognovisti omnia novissima, et antiqua: tu formasti me, et posuisti super me manum tuam.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Mirabilis facta est scientia tua ex me: confortata est, et non potero ad eam.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Quo ibo a Spiritu tuo? et quo a facie tua fugiam?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
Si ascendero in cælum, tu illic es: si descendero in infernum, ades. (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
Si sumpsero pennas meas diluculo, et habitavero in extremis maris:
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Etenim illuc manus tua deducet me: et tenebit me dextera tua.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
Et dixi: Forsitan tenebræ conculcabunt me: et nox illuminatio mea in deliciis meis.
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Quia tenebræ non obscurabuntur a te, et nox sicut dies illuminabitur: sicut tenebræ eius, ita et lumen eius.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
Quia tu possedisti renes meos: suscepisti me de utero matris meæ.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
Confitebor tibi quia terribiliter magnificatus es: mirabilia opera tua, et anima mea cognoscit nimis.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
Non est occultatum os meum a te, quod fecisti in occulto: et substantia mea in inferioribus terræ.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Imperfectum meum viderunt oculi tui, et in libro tuo omnes scribentur: dies formabuntur, et nemo in eis.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
Mihi autem nimis honorificati sunt amici tui, Deus: nimis confortatus est principatus eorum.
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
Dinumerabo eos, et super arenam multiplicabuntur: exurrexi, et adhuc sum tecum.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
Si occideris Deus peccatores: viri sanguinum declinate a me:
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
Quia dicitis in cogitatione: accipient in vanitate civitates tuas.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Nonne qui oderunt te Domine, oderam: et super inimicos tuos tabescebam?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
Perfecto odio oderam illos: et inimici facti sunt mihi.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Proba me Deus, et scito cor meum: interroga me, et cognosce semitas meas.
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
Et vide, si via iniquitatis in me est: et deduc me in via æterna.

< Zabura 139 >