< Zabura 135 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Let the Lord be praised. O you servants of the Lord, give praise to the name of the Lord.
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
You who are in the house of the Lord, and in the open spaces of the house of our God,
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Give praise to Jah, for he is good: make melody to his name, for it is pleasing.
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
For the Lord has taken Jacob for himself, and Israel for his property.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
I know that the Lord is great, and that our Lord is greater than all other gods.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
The Lord has done whatever was pleasing to him, in heaven, and on the earth, in the seas and in all the deep waters.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
He makes the mists go up from the ends of the earth; he makes thunder-flames for the rain; he sends out the winds from his store-houses.
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
He put to death the first-fruits of Egypt, of man and of beast.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
He sent signs and wonders among you, O Egypt, on Pharaoh, and on all his servants.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
He overcame great nations, and put strong kings to death;
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Sihon, king of the Amorites, and Og, king of Bashan, and all the kingdoms of Canaan;
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
And gave their land for a heritage, even for a heritage to Israel his people.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
O Lord, your name is eternal; and the memory of you will have no end.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
For the Lord will be judge of his people's cause; his feelings will be changed to his servants.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
The images of the nations are silver and gold, the work of men's hands.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
They have mouths, but no voice, they have eyes, but they do not see;
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
They have ears, but no hearing; and there is no breath in their mouths.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Those who make them are like them; and so is everyone who puts his hope in them.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Give praise to the Lord, O children of Israel: give praise to the Lord, O sons of Aaron:
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Give praise to the Lord, O sons of Levi: let all the worshippers of the Lord give him praise.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Praise be to the Lord out of Zion, even to the Lord whose house is in Jerusalem, Let the Lord be praised.

< Zabura 135 >