< Zabura 119 >

1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
ALEPH. Bienheureux [sont] ceux qui sont intègres en leur voie, qui marchent en la Loi de l'Eternel.
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Bienheureux sont ceux qui gardent ses témoignages, et qui le cherchent de tout leur cœur;
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
Qui aussi ne font point d'iniquité, [et] qui marchent dans ses voies.
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Tu as donné tes commandements afin qu'on les garde soigneusement.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Qu'il te plaise, ô Dieu! que mes voies soient bien dressées, pour garder tes statuts.
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Et je ne rougirai point de honte, quand je regarderai à tous tes commandements.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
Je te célébrerai avec droiture de cœur, quand j'aurai appris les ordonnances de ta justice.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Je veux garder tes statuts; ne me délaisse point entièrement.
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
BETH. Par quel moyen le jeune homme rendra-t-il pure sa voie? Ce sera en y prenant garde selon ta parole.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
Je t'ai recherché de tout mon cœur, ne me fais point fourvoyer de tes commandements.
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
J'ai serré ta parole dans mon cœur, afin que je ne pèche point contre toi.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Eternel! tu es béni; enseigne-moi tes statuts.
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
J'ai raconté de mes lèvres toutes les ordonnances de ta bouche.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
Je me suis réjoui dans le chemin de tes témoignages, comme si j'eusse eu toutes les richesses du monde.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
Je m'entretiendrai de tes commandements, et je regarderai à tes sentiers.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
Je prends plaisir à tes statuts, et je n'oublierai point tes paroles.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
GUIMEL. Fais ce bien à ton serviteur que. je vive, et je garderai ta parole.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Dessille mes yeux, afin que je regarde aux merveilles de ta Loi.
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
Je suis voyageur en la terre; ne cache point de moi tes commandements.
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
Mon âme est toute embrasée de l'affection qu'elle a de tout temps pour tes ordonnances.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Tu as rudement tancé les orgueilleux maudits, qui se détournent de tes commandements.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Ote de dessus moi l'opprobre et le mépris; car j'ai gardé tes témoignages.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Même les principaux se sont assis [et] ont parlé contre moi, pendant que ton serviteur s'entretenait de tes statuts.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Aussi tes témoignages [sont] mes plaisirs, [et] les gens de mon conseil.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
DALETH. Mon âme est attachée à la poudre; fais-moi revivre selon ta parole.
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
Je t'ai déclaré au long mes voies, et tu m'as répondu; enseigne-moi tes statuts.
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Fais-moi entendre la voie de tes commandements, et je discourrai de tes merveilles.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
Mon âme s'est fondue d'ennui, relève moi selon tes paroles.
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Eloigne de moi la voie du mensonge, et me donne gratuitement ta Loi.
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
J'ai choisi la voie de la vérité, et je me suis proposé tes ordonnances.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
J'ai été attaché à tes témoignages, ô Eternel! ne me fais point rougir de honte.
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
Je courrai par la voie de tes commandements, quand tu auras mis mon cœur au large.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
HE. Eternel, enseigne-moi la voie de tes statuts, et je la garderai jusques au bout.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Donne-moi de l'intelligence; je garderai ta Loi, et je l'observerai de tout [mon] cœur.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Fais-moi marcher dans le sentier de tes commandements; car j'y prends plaisir.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Incline mon cœur à tes témoignages, et non point au gain déshonnête.
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Détourne mes yeux qu'ils ne regardent à la vanité; fais-moi revivre par le moyen de tes voies.
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Ratifie ta parole à ton serviteur, qui est adonné à ta crainte.
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Ote mon opprobre, lequel j'ai craint; car tes ordonnances sont bonnes.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Voici, je suis affectionné à tes commandements; fais-moi revivre par ta justice.
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
VAU. Et que tes faveurs viennent sur moi, ô Eternel! [et] ta délivrance aussi, selon ta parole;
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
Afin que j'aie de quoi répondre à celui qui me charge d'opprobre: car j'ai mis ma confiance en ta parole.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
Et n'arrache point de ma bouche la parole de vérité; car je me suis attendu à tes ordonnances.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
Je garderai continuellement ta Loi, à toujours et à perpétuité.
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
Je marcherai au large, parce que j'ai recherché tes commandements.
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
Je parlerai de tes témoignages devant les Rois, et je ne rougirai point de honte.
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
Et je prendrai mon plaisir en tes commandements, que j'ai aimés;
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
Même j'étendrai mes mains vers tes commandements, que j'ai aimés; et je m'entretiendrai de tes statuts.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
ZAIN. Souviens-toi de la parole donnée à ton serviteur, à laquelle tu as fait que je me suis attendu.
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
C'[est] ici ma consolation dans mon affliction, que ta parole m'a remis en vie.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
Les orgueilleux se sont fort moqués de moi, [mais] je ne me suis point dé tourné de ta Loi.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
Eternel, je me suis souvenu des jugements d'ancienneté, et je me suis consolé [en eux].
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
L'horreur m'a saisi, à cause des méchants qui ont abandonné ta Loi.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Tes statuts ont été le sujet de mes cantiques dans la maison où j ai demeuré comme voyageur.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
Eternel, je me suis souvenu de ton Nom pendant la nuit, et j'ai gardé ta Loi.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
Cela m'est arrivé, parce que je gardais tes commandements.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
HETH. Ô Eternel! j'ai conclu que ma portion était de garder tes paroles.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
Je t'ai supplié de tout mon cœur, aie pitié de moi selon ta parole.
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
J'ai fait le compte de mes voies, et j'ai rebroussé chemin vers tes témoignages.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
Je me suis hâté, je n'ai point différé à garder tes commandements.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
Les troupes des méchants m'ont pillé, [mais] je n'ai point oublié ta Loi.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
Je me lève à minuit pour te célébrer à cause des ordonnances de ta justice.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
Je m'accompagne de tous ceux qui te craignent, et qui gardent tes commandements.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Eternel, la terre est pleine de tes faveurs; enseigne-moi tes statuts.
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
TETH. Eternel, tu as fait du bien à ton serviteur selon ta parole.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Enseigne-moi d'avoir bon sens et connaissance, car j'ai ajouté foi à tes commandements.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Avant que je fusse affligé, j'allais à travers champs; mais maintenant j'observe ta parole.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Tu [es] bon et bienfaisant, enseigne-moi tes statuts.
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
Les orgueilleux ont forgé des faussetés contre moi; [mais] je garderai de tout mon cœur tes commandements.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Leur cœur est comme figé de graisse; mais moi, je prends plaisir en ta Loi.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
Il m'est bon que j'aie été affligé, afin que j'apprenne tes statuts.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
La Loi [que tu as prononcée] de ta bouche, m'[est] plus précieuse que mille [pièces] d'or ou d'argent.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
JOD. Tes mains m'ont fait, et façonné; rends-moi entendu, afin que j'apprenne tes commandements.
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
Ceux qui te craignent me verront, et se réjouiront; parce que je me suis attendu à ta parole.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
Je connais, ô Eternel! que tes ordonnances ne sont que justice; et que tu m'as affligé suivant ta fidélité.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Je te prie, que ta miséricorde me console, selon ta parole [adressée] à ton serviteur.
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Que tes compassions se répandent sur moi, et je vivrai; car ta Loi est tout mon plaisir.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Que les orgueilleux rougissent de honte, de ce qu ils m'ont renversé sans sujet; [mais] moi, je discourrai de tes commandements.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Que ceux qui te craignent, et ceux qui connaissent tes témoignages, reviennent vers moi.
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Que mon cœur soit intègre dans tes statuts, afin que je ne rougisse point de honte.
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
CAPH. Mon âme s'est consumée en attendant ta délivrance; je me suis attendu à ta parole.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Mes yeux se sont épuisés [en attendant] ta parole, lorsque j'ai dit: quand me consoleras-tu?
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
Car je suis devenu comme un outre mis à la fumée, [et je] n'ai point oublié tes statuts.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
Combien [ont à durer] les jours de ton serviteur? Quand jugeras-tu ceux qui me poursuivent?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
Les orgueilleux m'ont creusé des fosses, ce qui n'est pas selon ta Loi.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
Tous tes commandements [ne sont que] fidélité; on me persécute sans cause; aide-moi.
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
On m'a presque réduit à rien, [et] mis par terre: mais je n'ai point abandonné tes commandements.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Fais-moi revivre selon ta miséricorde, et je garderai le témoignage de ta bouche.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
LAMED. Ô Eternel! ta parole subsiste à toujours dans les cieux.
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
Ta fidélité dure d'âge en âge; tu as établi la terre, et elle demeure ferme.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
[Ces choses] subsistent aujourd'hui selon tes ordonnances; car toutes choses te servent.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
N'eût été que ta Loi a été tout mon plaisir, j'eusse déjà péri dans mon affliction.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
Je n'oublierai jamais tes commandements; car tu m'as fait revivre par eux.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
Je suis à toi, sauve-moi; car j'ai recherché tes commandements.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
Les méchants m'ont attendu, pour me faire périr; [mais] je me suis rendu attentif à tes témoignages.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
J'ai vu un bout dans toutes les choses les plus parfaites; [mais] ton commandement [est] d'une très-grande étendue.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
MEM. Ô combien j'aime ta Loi! c'est ce dont je m'entretiens tout le jour.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Tu m'as rendu plus sage par tes commandements, que ne sont mes ennemis; parce que tes commandements sont toujours avec moi.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
J'ai surpassé en prudence tous ceux qui m'avaient enseigné, parce que tes témoignages son mon entretien.
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
Je suis devenu plus intelligent que les anciens, parce que j'ai observé tes commandements.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
J'ai gardé mes pieds de toute mauvaise voie, afin que j'observasse ta parole.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
Je ne me suis point détourné de tes ordonnances, parce que tu me [les] as enseignées.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
Ô que ta parole a été douce à mon palais! plus douce que le miel à ma bouche.
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
Je suis devenu intelligent par tes commandements, c'est pourquoi j'ai haï toute voie de mensonge.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
NUN. Ta parole est une lampe à mon pied, et une lumière à mon sentier.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
J'ai juré, et je le tiendrai, d'observer les ordonnances de ta justice.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
Eternel, je suis extrêmement affligé, fais-moi revivre selon ta parole.
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Eternel, je te prie, aie pour agréables les oblations volontaires de ma bouche, et enseigne-moi tes ordonnances.
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
Ma vie a été continuellement en danger, toutefois je n'ai point oublié ta Loi.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
Les méchants m'ont tendu des piéges, toutefois je ne me suis point égaré de tes commandements.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
J'ai pris pour héritage perpétuel tes témoignages; car ils sont la joie de mon cœur.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
J'ai incliné mon cœur à accomplir toujours tes statuts jusques au bout.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
SAMECH. J'ai eu en haine les pensées diverses, mais j'ai aimé ta Loi.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Tu es mon asile et mon bouclier, je me suis attendu à ta parole.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Méchants, retirez-vous de moi, et je garderai les commandements de mon Dieu.
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Soutiens-moi suivant ta parole, et je vivrai; et ne me fais point rougir de honte en me refusant ce que j'espérais.
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Soutiens-moi, et je serai en sûreté, et j'aurai continuellement les yeux sur tes statuts.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Tu as foulé aux pieds tous ceux qui se détournent de tes statuts; car le mensonge est le moyen dont ils se servent pour tromper.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Tu as réduit à néant tous les méchants de la terre, comme n'étant qu'écume; c'est pourquoi j'ai aimé tes témoignages.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
Ma chair a frémi de la frayeur que j'ai de toi, et j'ai craint tes jugements.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
HAJIN. J'ai exercé jugement et justice, ne m'abandonne point à ceux qui me font tort.
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Sois le pleige de ton serviteur pour son bien; [et ne permets pas] que je sois opprimé par les orgueilleux,
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Mes yeux se sont épuisés en attendant ta délivrance, et la parole de ta justice.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Agis envers ton serviteur suivant ta miséricorde et m'enseigne tes statuts.
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Je suis ton serviteur, rends-moi intelligent, et je connaîtrai tes témoignages.
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
Il est temps que l'Eternel opère; ils ont aboli ta Loi.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
C'est pourquoi j'ai aimé tes commandements, plus que l'or, même plus que le fin or.
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
C'est pourquoi j'ai estimé droits tous les commandements que tu donnes de toutes choses, [et] j'ai eu en haine toute voie de mensonge.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
PE. Tes témoignages sont des choses merveilleuses; c'est pourquoi mon âme les a gardés.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
L'entrée de tes paroles illumine, [et] donne de l'intelligence aux simples.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
J'ai ouvert ma bouche, et j'ai soupiré; car j'ai souhaité tes commandements.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Regarde-moi, et aie pitié de moi, selon que tu as ordinairement compassion de ceux qui aiment ton Nom.
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Affermis mes pas sur ta parole, et que l'iniquité n'ait point d'empire sur moi.
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Délivre-moi de l'oppression des hommes, afin que je garde tes commandements.
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Fais luire ta face sur ton serviteur, et m'enseigne tes statuts.
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Mes yeux se sont fondus en ruisseaux d'eau, parce qu'on n'observe point ta Loi.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
TSADE. Tu es juste, ô Eternel! et droit en tes jugements.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Tu as ordonné tes témoignages comme une chose juste, et souverainement ferme.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
Mon zèle m'a miné; parce que mes adversaires ont oublié tes paroles.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Ta parole est souverainement raffinée, c'est pourquoi ton serviteur l'aime.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Je suis petit et méprisé, [toutefois] je n'oublie point tes commandements.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Ta justice est une justice à toujours, et ta Loi est la vérité.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
La détresse et l'angoisse m'avaient rencontré; [mais] tes commandements sont mes plaisirs.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Tes témoignages ne sont que justice à toujours; donne m'en l’intelligence, afin que je vive.
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
KOPH. J'ai crié de tout mon cœur, réponds-moi, ô Eternel! [et] je garderai tes statuts.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
J'ai crié vers toi; sauve-moi, afin que j'observe tes témoignages.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
J'ai prévenu le point du jour, et j'ai crié; je me suis attendu à ta parole.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Mes yeux ont prévenu les veilles de la nuit pour méditer la parole.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Ecoute ma voix selon ta miséricorde: ô Eternel! fais-moi revivre selon ton ordonnance.
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
Ceux qui sont adonnés à des machinations se sont approchés de moi, [et] ils se sont éloignés de ta Loi.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Eternel, tu es aussi près de moi; et tous tes commandements ne sont que vérité.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
J'ai connu dès longtemps touchant tes témoignages, que tu les as fondés pour toujours.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
RESCH. Regarde mon affliction, et m'en retire; car je n'ai point oublié ta Loi.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Soutiens ma cause, et me rachète; fais-moi revivre suivant ta parole.
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
La délivrance est loin des méchants; parce qu'ils n'ont point recherché tes statuts.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Tes compassions sont en grand nombre, ô Eternel! fais-moi revivre selon tes ordonnances.
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Ceux qui me persécutent et qui me pressent, [sont] en grand nombre: [toutefois] je ne me suis point détourné de tes témoignages.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
J'ai jeté les yeux sur les perfides et j'ai été rempli de tristesse de ce qu'ils n'observaient point ta parole.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
Regarde combien j'ai aimé tes commandements; Eternel! fais-moi revivre selon ta miséricorde.
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
Le principal point de ta parole est la vérité, et toute l'ordonnance de ta justice est à toujours.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
SCIN. Les principaux du peuple m'ont persécuté sans sujet; mais mon cœur a été effrayé à cause de ta parole.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
Je me réjouis de ta parole, comme ferait celui qui aurait trouvé un grand butin.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
J'ai eu en haine et en abomination le mensonge; j'ai aimé ta Loi.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Sept fois le jour je te loue à cause des ordonnances de ta justice.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Il y a une grande paix pour ceux qui aiment ta Loi, et rien ne peut les renverser.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
Eternel, j'ai espéré en ta délivrance, et j'ai fait tes commandements.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
Mon âme a observé tes témoignages, et je les ai souverainement aimés.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
J'ai observé tes commandements et tes témoignages; car toutes mes voies sont devant toi.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
THAU. Eternel, que mon cri approche de ta présence; rends-moi intelligent selon ta parole.
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Que ma supplication vienne devant toi; délivre-moi selon ta parole.
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
Mes lèvres publieront ta louange, quand tu m'auras enseigné tes statuts.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
Ma langue ne s'entretiendra que de ta parole; parce que tous tes commandements ne sont que justice.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Que ta main me soit en aide, parce que j'ai choisi tes commandements.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
Eternel, j'ai souhaité ta délivrance, et ta Loi est tout mon plaisir.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Que mon âme vive, afin qu'elle te loue; et fais que tes ordonnances me soient en aide.
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
J'ai été égaré comme la brebis perdue; cherche ton serviteur; car je n'ai point mis en oubli tes commandements.

< Zabura 119 >