< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
To the Overseer. — A Psalm of David. O God of my praise, be not silent,
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
For the mouth of wickedness, and the mouth of deceit, Against me they have opened, They have spoken with me — A tongue of falsehood, and words of hatred!
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
They have compassed me about, And they fight me without cause.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
For my love they oppose me, and I — prayer!
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
And they set against me evil for good, And hatred for my love.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Appoint Thou over him the wicked, And an adversary standeth at his right hand.
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
In his being judged, he goeth forth wicked, And his prayer is for sin.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
His days are few, his oversight another taketh,
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
His sons are fatherless, and his wife a widow.
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
And wander continually do his sons, Yea, they have begged, And have sought out of their dry places.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
An exactor layeth a snare for all that he hath, And strangers spoil his labour.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
He hath none to extend kindness, Nor is there one showing favour to his orphans.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
His posterity is for cutting off, In another generation is their name blotted out.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
The iniquity of his fathers Is remembered unto Jehovah, And the sin of his mother is not blotted out.
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
They are before Jehovah continually, And He cutteth off from earth their memorial.
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
Because that he hath not remembered to do kindness, And pursueth the poor man and needy, And the smitten of heart — to slay,
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
And he loveth reviling, and it meeteth him, And he hath not delighted in blessing, And it is far from him.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
And he putteth on reviling as his robe, And it cometh in as water into his midst, And as oil into his bones.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
It is to him as apparel — he covereth himself, And for a continual girdle he girdeth it on.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
This [is] the wage of mine accusers from Jehovah, And of those speaking evil against my soul.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
And Thou, O Jehovah Lord, Deal with me for Thy name's sake, Because Thy kindness [is] good, deliver me.
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
For I [am] poor and needy, And my heart hath been pierced in my midst.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
As a shadow when it is stretched out I have gone, I have been driven away as a locust.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
My knees have been feeble from fasting, And my flesh hath failed of fatness.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
And I — I have been a reproach to them, They see me, they shake their head.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Help me, O Jehovah my God, Save me, according to Thy kindness.
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
And they know that this [is] Thy hand, Thou, O Jehovah, Thou hast done it.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
They revile, and Thou dost bless, They have risen, and are ashamed, And Thy servant doth rejoice.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Mine accusers put on blushing, and are covered, As an upper robe [is] their shame.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
I thank Jehovah greatly with my mouth, And in the midst of many I praise Him,
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
For He standeth at the right hand of the needy, To save from those judging his soul.

< Zabura 109 >