< Zabura 107 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
O give thanks unto the LORD, for [he is] good: for his mercy [endureth] for ever.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Let the redeemed of the LORD say [so], whom he hath redeemed from the hand of the enemy;
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
And gathered them out of the lands, from the east, and from the west, from the north, and from the south.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
They wandered in the wilderness in a solitary way; they found no city to dwell in.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Hungry and thirsty, their soul fainted in them.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Then they cried unto the LORD in their trouble, [and] he delivered them out of their distresses.
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
And he led them forth by the right way, that they might go to a city of habitation.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Oh that [men] would praise the LORD [for] his goodness, and [for] his wonderful works to the children of men!
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
For he satisfieth the longing soul, and filleth the hungry soul with goodness.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Such as sit in darkness and in the shadow of death, [being] bound in affliction and iron;
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Because they rebelled against the words of God, and contemned the counsel of the most High:
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Therefore he brought down their heart with labour; they fell down, and [there was] none to help.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cried unto the LORD in their trouble, [and] he saved them out of their distresses.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
He brought them out of darkness and the shadow of death, and brake their bands in sunder.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Oh that [men] would praise the LORD [for] his goodness, and [for] his wonderful works to the children of men!
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
For he hath broken the gates of brass, and cut the bars of iron in sunder.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Fools because of their transgression, and because of their iniquities, are afflicted.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Their soul abhorreth all manner of meat; and they draw near unto the gates of death.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cry unto the LORD in their trouble, [and] he saveth them out of their distresses.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
He sent his word, and healed them, and delivered [them] from their destructions.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Oh that [men] would praise the LORD [for] his goodness, and [for] his wonderful works to the children of men!
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
And let them sacrifice the sacrifices of thanksgiving, and declare his works with rejoicing.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
They that go down to the sea in ships, that do business in great waters;
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
These see the works of the LORD, and his wonders in the deep.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
For he commandeth, and raiseth the stormy wind, which lifteth up the waves thereof.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
They mount up to the heaven, they go down again to the depths: their soul is melted because of trouble.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
They reel to and fro, and stagger like a drunken man, and are at their wits’ end.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Then they cry unto the LORD in their trouble, and he bringeth them out of their distresses.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
He maketh the storm a calm, so that the waves thereof are still.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Then are they glad because they be quiet; so he bringeth them unto their desired haven.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Oh that [men] would praise the LORD [for] his goodness, and [for] his wonderful works to the children of men!
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Let them exalt him also in the congregation of the people, and praise him in the assembly of the elders.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
He turneth rivers into a wilderness, and the watersprings into dry ground;
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
A fruitful land into barrenness, for the wickedness of them that dwell therein.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
He turneth the wilderness into a standing water, and dry ground into watersprings.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
And there he maketh the hungry to dwell, that they may prepare a city for habitation;
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
And sow the fields, and plant vineyards, which may yield fruits of increase.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
He blesseth them also, so that they are multiplied greatly; and suffereth not their cattle to decrease.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Again, they are minished and brought low through oppression, affliction, and sorrow.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
He poureth contempt upon princes, and causeth them to wander in the wilderness, [where there is] no way.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Yet setteth he the poor on high from affliction, and maketh [him] families like a flock.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
The righteous shall see [it], and rejoice: and all iniquity shall stop her mouth.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Whoso [is] wise, and will observe these [things], even they shall understand the lovingkindness of the LORD.

< Zabura 107 >