< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
主をほめたたえよ。主に感謝せよ、主は恵みふかく、そのいつくしみはとこしえに絶えることがない。
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
だれが主の大能のみわざを語り、その誉をことごとく言いあらわすことができようか。
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
公正を守る人々、常に正義を行う人はさいわいである。
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
主よ、あなたがその民を恵まれるとき、わたしを覚えてください。あなたが彼らを救われるとき、わたしを助けてください。
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
そうすれば、わたしはあなたの選ばれた者の繁栄を見、あなたの国民の喜びをよろこび、あなたの嗣業と共に誇ることができるでしょう。
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
われらは先祖たちと同じく罪を犯した。われらは不義をなし、悪しきことを行った。
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
われらの先祖たちはエジプトにいたとき、あなたのくすしきみわざに心を留めず、あなたのいつくしみの豊かなのを思わず、紅海で、いと高き神にそむいた。
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
けれども主はその大能を知らせようと、み名のために彼らを救われた。
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
主は紅海をしかって、それをかわかし、彼らを導いて荒野を行くように、淵を通らせられた。
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
こうして主は彼らをあだの手から救い、敵の力からあがなわれた。
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
水が彼らのあだをおおったので、そのうち、ひとりも生き残った者はなかった。
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
このとき彼らはそのみ言葉を信じ、その誉を歌った。
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
しかし彼らはまもなくそのみわざを忘れ、その勧めを待たず、
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
野でわがままな欲望を起し、荒野で神を試みた。
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
主は彼らにその求めるものを与えられたが、彼らのうちに病気を送って、やせ衰えさせられた。
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
人々が宿営のうちでモーセをねたみ、主の聖者アロンをねたんだとき、
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
地が開けてダタンを飲み、アビラムの仲間をおおった。
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
火はまたこの仲間のうちに燃え起り、炎は悪しき者を焼きつくした。
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
彼らはホレブで子牛を造り、鋳物の像を拝んだ。
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
彼らは神の栄光を草を食う牛の像と取り替えた。
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
彼らは、エジプトで大いなる事をなし、ハムの地でくすしきみわざをなし、紅海のほとりで恐るべき事をなされた救主なる神を忘れた。
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
それゆえ、主は彼らを滅ぼそうと言われた。しかし主のお選びになったモーセは破れ口で主のみ前に立ち、み怒りを引きかえして、滅びを免れさせた。
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
彼らは麗しい地を侮り、主の約束を信ぜず、
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
またその天幕でつぶやき、主のみ声に聞き従わなかった。
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
それゆえ、主はみ手をあげて、彼らに誓い、彼らを荒野で倒れさせ、
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
またその子孫を、もろもろの国民のうちに追い散らし、もろもろの地に彼らをまき散らそうとされた。
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
また彼らはペオルのバアルを慕って、死んだ者にささげた、いけにえを食べた。
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
彼らはそのおこないをもって主を怒らせたので、彼らのうちに疫病が起った。
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
その時ピネハスが立って仲裁にはいったので、疫病はやんだ。
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
これによってピネハスはよろず代まで、とこしえに義とされた。
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
彼らはまたメリバの水のほとりで主を怒らせたので、モーセは彼らのために災にあった。
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
これは彼らが神の霊にそむいたとき、彼がそのくちびるで軽率なことを言ったからである。
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
彼らは主が命じられたもろもろの民を滅ぼさず、
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
かえってもろもろの国民とまじってそのわざにならい、
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
自分たちのわなとなった偶像に仕えた。
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
彼らはそのむすこ、娘たちを悪霊にささげ、
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
罪のない血、すなわちカナンの偶像にささげたそのむすこ、娘たちの血を流した。こうして国は血で汚された。
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
このように彼らはそのわざによっておのれを汚し、そのおこないによって姦淫をなした。
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
それゆえ、主の怒りがその民にむかって燃え、その嗣業を憎んで、
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
彼らをもろもろの国民の手にわたされた。彼らはおのれを憎む者に治められ、
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
その敵にしえたげられ、その力の下に征服された。
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
主はしばしば彼らを助けられたが、彼らははかりごとを設けてそむき、その不義によって低くされた。
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
それにもかかわらず、主は彼らの叫びを聞かれたとき、その悩みをかえりみ、
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
その契約を彼らのために思い出し、そのいつくしみの豊かなるにより、みこころを変えられ、
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
彼らをとりこにした者どもによって、あわれまれるようにされた。
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
われらの神、主よ、われらを救って、もろもろの国民のなかから集めてください。われらはあなたの聖なるみ名に感謝し、あなたの誉を誇るでしょう。
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
イスラエルの神、主はとこしえからとこしえまでほむべきかな。すべての民は「アァメン」ととなえよ。主をほめたたえよ。

< Zabura 106 >