< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Hallelujah! Bekennet Jehovah, denn Er ist gut, denn Seine Barmherzigkeit ist in Ewigkeit.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Wer kann aussagen die Machttaten Jehovahs, kann hören lassen all Sein Lob?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Selig, die das Recht halten und Gerechtigkeit tun alle Zeit!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Gedenke mein, Jehovah, mit dem Wohlgefallen für Dein Volk, und suche mich heim mit Deinem Heil.
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Daß ich sehe das Gute Deiner Auserwählten, daß ich fröhlich sei in der Fröhlichkeit Deiner Völkerschaften, mich rühme mit Deinem Erbe.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Wir sündigten mit unseren Vätern, wir haben Missetat, Ungerechtigkeit begangen.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Unsere Väter in Ägypten begriffen Deine Wunder nicht, gedachten nicht Deiner vielen Barmherzigkeit, und sie widersetzten sich am Meer, am Meere des Schilfs.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Er aber rettete sie um Seines Namens willen, um Seine Macht kund zu tun.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Und Er bedrohte das Schilfmeer, und es trocknete aus, und Er ließ sie durch Abgründe gehen wie durch die Wüste.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Und Er rettete sie aus des Hassers Hand, und aus des Feindes Hand erlöste Er sie.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Und Wasser bedeckten ihre Dränger, nicht einer blieb von ihnen übrig.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Und sie glaubten an Seine Worte, sie sangen Sein Lob.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Eilig hatten Seine Werke sie vergessen, warteten nicht auf Seinen Ratschluß.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Und es gelüstete sie in der Wüste ein Gelüste, und sie versuchten Gott im Wüstenland.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Und Er gab ihnen ihr Erbetenes, sandte aber Magerkeit in ihre Seele.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Und sie eiferten wider Mose in dem Lager, wider Aharon, den Heiligen Jehovahs.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Die Erde tat sich auf und verschlang Dathan und überdeckte Abirams Gemeinde.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Und es brannte Feuer in ihrer Gemeinde, und die Flamme entflammte die Ungerechten.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Am Choreb machten sie ein Kalb und beteten das Gußbild an,
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Und sie vertauschten ihre Herrlichkeit mit dem Vorbilde eines Ochsen, der das Kraut frißt.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Sie vergaßen des Gottes, Der sie gerettet, Der in Ägypten Großes tat.
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Wunder im Lande Cham, Furchtbares an dem Meere des Schilfs.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Und Er sagte, Er wollte sie vernichten, wenn Mose, Sein Auserwählter, nicht vor Ihm vor den Riß gestanden wäre, um Seinen Grimm vom Verderben zurückzuwenden.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Und sie verschmähten das begehrte Land, sie glaubten Seinem Worte nicht.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Und sie beschwerten sich in ihren Zelten, und hörten nicht auf Jehovahs Stimme.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Und Er hob Seine Hand auf wider sie, sie zu fällen in der Wüste.
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
Und ihren Samen unter die Völkerschaften fallen zu lassen, und sie in die Länder zu zersprengen.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Und sie klammerten sich an Baal-Peor und aßen die Opfer der Toten.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Und reizten Ihn durch ihr Tun, daß eine Plage ausbrach unter ihnen.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Und Phinechas stand da und schlichtete, und der Plage ward Einhalt getan.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Und ihm ward es zur Gerechtigkeit gerechnet ins Geschlecht und Geschlecht in Ewigkeit.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Und sie reizten zur Entrüstung am Wasser Meribah, und es war übel mit Mose um ihretwillen.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Denn sie erbitterten den Geist ihm, und es entfuhr seinen Lippen.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Sie vernichteten die Völker nicht, wie Jehovah zu ihnen gesprochen hatte,
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Und vermengten sich mit den Völkerschaften und lernten ihr Tun;
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Und sie dienten ihren Götzenbildern und sie wurden ihnen zum Fallstrick.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Und sie opferten den Dämonen ihre Söhne und Töchter.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Und sie vergossen unschuldig Blut, das Blut ihrer Söhne und ihrer Töchter, die sie den Götzenbildern Kanaans opferten, und das Land ward durch Blut entheiligt.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Und sie verunreinigten sich durch ihre Werke, und buhlten durch ihr Tun.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Und es entbrannte Jehovahs Zorn wider Sein Volk, und Sein Erbe ward Ihm zum Greuel.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Und Er gab sie in der Völkerschaften Hand, und ihre Hasser herrschten über sie.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Und ihre Feinde unterdrückten sie, und sie wurden unter ihre Hand gebeugt.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Viel Male errettete Er sie, doch sie widersetzten sich in ihrem Ratschlusse, und schwanden dahin in ihrer Missetat.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Und Er sah ihre Drangsal, wie Er ihren Angstschrei hörte.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Und Er gedachte ihnen an Seinen Bund, und es gereute Ihn nach Seiner vielen Barmherzigkeit.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Und Er ließ sie Erbarmen finden vor allen, die sie gefangen führten.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Rette uns, Jehovah, unser Gott, und bringe uns zusammen aus den Völkerschaften, auf daß wir bekennen den Namen Deiner Heiligkeit und preisen Dein Lob.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Gesegnet sei Jehovah, der Gott Israels, von Ewigkeit und zu Ewigkeit! und alles Volk spreche: Amen. Hallelujah!

< Zabura 106 >