< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Give thanks to the Lord, call on his name: make known his deeds among the nations.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Sing to him, make music to him, tell of all his wondrous works.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Make your boast in his holy name, be glad at heart, you who seek the Lord.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Seek after the Lord and his strength, seek his face evermore.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Remember the wonders he did, his portents, the judgments he uttered,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
you who are offspring of Abraham, his servant, the children of Jacob, his chosen ones.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
He is the Lord our God: in all the earth are his judgments.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
He remembers forever his covenant, his promise for a thousand generations
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
The covenant he made with Abraham, the oath he swore to Isaac,
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
and confirmed as a statute to Jacob, a pact everlasting to Israel
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
to give them the land of Canaan as the lot which they should inherit.
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
And when they were very few, few and but pilgrims therein,
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
wandering from nation to nation, journeying from people to people,
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
he allowed no one to oppress them, even punishing kings for their sakes.
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
He forbade them to touch his anointed, or do any hurt to his prophets.
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
When he called down famine on the land, and cut off the bread which sustained them,
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
he sent before them a man, Joseph, who was sold as a slave.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
His feet were galled with fetters, he was laid in chains of iron,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
till the time that his word came to pass, the word of the Lord that had tried him.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
The king sent and freed him, the ruler of nations released him.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
He made him lord of his household, and ruler of all his possessions,
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
to admonish his princes at will and instruct his elders in wisdom.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Thus Israel came into Egypt, Jacob sojourned in the land of Ham.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
His people he made very fruitful, and mightier than their foes.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
He inspired them to hate his people, and to deal with his servants craftily.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
He sent his servant Moses, and Aaron whom he had chosen,
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
portents he wrought in Egypt, and signs in the land of Ham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Darkness he sent, and it fell: yet they gave no heed to his word.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
He turned their waters into blood, thus causing their fish to die.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Their land was alive with frogs, swarming even in the royal chambers.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
At his command came flies, and lice in all their borders.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
He gave them hail for rain and fire that flashed through the land,
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
smiting their vines and figs, breaking the trees of their border.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
At his command came locusts, young locusts beyond all counting,
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
which ate every herb in the land, ate up, too, the fruit of their ground.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
He struck down in their land all the firstborn, the firstlings of all their strength
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Then forth he led Israel with silver and gold, and among his tribes no one was weary.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egypt was glad when they left, for terror had fallen upon them.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
He spread out a cloud to screen them, and fire to give light in the night.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
He sent quails at their entreaty, and heavenly bread in abundance.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
He opened the rock; waters gushed: in the desert they ran like a river.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
For he remembered his holy promise to Abraham his servant.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
So he led out his people with joy, his elect with a ringing cry.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
And he gave them the lands of the nations, the fruit of their toil for possession,
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
that so they might keep his statutes, and be of his laws observant. Hallelujah.

< Zabura 105 >