< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Give thanks to Jehovah. Call on his name. Make his deeds known among the peoples.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Sing to him, sing praises to him. Tell of all his marvelous works.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Glory in his holy name. Let the heart of those who seek Jehovah rejoice.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Seek Jehovah and his strength. Seek his face forever more.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Remember his marvelous works that he has done; his wonders, and the judgments of his mouth,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
you offspring of Abraham, his servant, you descendants of Jacob, his chosen ones.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
He is Jehovah, our God. His judgments are in all the earth.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
He has remembered his covenant forever, the word which he commanded to a thousand generations,
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
the covenant which he made with Abraham, his oath to Isaac,
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
and confirmed the same to Jacob for a statute; to Israel for an everlasting covenant,
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
saying, "To you I will give the land of Canaan, the lot of your inheritance;"
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
when they were but a few men in number, yes, very few, and foreigners in it.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
They went about from nation to nation, from one kingdom to another people.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
He allowed no one to do them wrong. Yes, he reproved kings for their sakes,
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
"Do not touch my anointed ones. Do my prophets no harm."
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
He called for a famine on the land. He destroyed the food supplies.
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
He sent a man ahead of them, Joseph, sold as a slave.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
They bruised his feet with shackles. His neck was locked in irons,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
until the time that his word happened, and Jehovah's word proved him true.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
The king sent and freed him; even the ruler of peoples, and let him go free.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
He made him lord of his house, and ruler of all of his possessions;
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
to discipline his princes at his pleasure, and to teach his elders wisdom.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Israel also came into Egypt. Jacob sojourned in the land of Ham.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
He increased his people greatly, and made them stronger than their adversaries.
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
He turned their heart to hate his people, to conspire against his servants.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
He sent Moses, his servant, and Aaron, whom he had chosen.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
They performed miracles among them, and wonders in the land of Ham.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
He sent darkness, and made it dark, but they rebelled against his words.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
He turned their waters into blood, and killed their fish.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Their land swarmed with frogs, even in the chambers of their kings.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
He spoke, and swarms of flies came, and gnats in all their territory.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
He gave them hail for rain, flaming fire in their land.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
He struck their vines and also their fig trees, and shattered the trees of their country.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
He spoke, and the locusts came, and the grasshoppers, without number,
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
ate up every plant in their land; and ate up the fruit of their ground.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
He struck also all the firstborn in their land, the first fruits of all their manhood.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
And he brought them out with silver and gold, and there was no one among their tribes who stumbled.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egypt was glad when they departed, for the fear of them had fallen on them.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
He spread a cloud for a covering, fire to give light in the night.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
They asked, and he brought quails, and satisfied them with the bread of the sky.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
He opened the rock, and waters gushed out. They ran as a river in the dry places.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
For he remembered his holy word, and Abraham, his servant.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
He brought forth his people with joy, his chosen with singing.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
He gave them the lands of the nations. They took the labor of the peoples in possession,
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
that they might keep his statutes, and observe his laws. Praise JAH.

< Zabura 105 >