< Zabura 104 >

1 Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Благосиљај, душо моја, Господа! Господе, Боже мој, велик си веома, обукао си се у величанство и красоту.
2 Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
Обукао си светлост као хаљину, разапео небо као шатор;
3 ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Водом си покрио дворове своје, облаке начинио си да су Ти кола, идеш на крилима ветреним.
4 Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
Чиниш ветрове да су Ти анђели, пламен огњени да су Ти слуге.
5 Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
Утврдио си земљу на темељима њеним, да се не помести на век века.
6 Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
Безданом као хаљином оденуо си је; на горама стоје воде.
7 Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
Од претње Твоје беже, од громовног гласа Твог теку.
8 suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
Излазе на горе и силазе у долине, на место које си им утврдио.
9 Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
Поставио си међу, преко које не прелазе, и не враћају се да покрију земљу.
10 Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
Извео си изворе по долинама, између гора теку воде.
11 Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
Напајају све звери пољске; дивљи магарци гасе жеђ своју.
12 Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
На њима птице небеске живе; кроз гране разлеже се глас њихов.
13 Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
Напајаш горе с висина својих, плодовима дела Твојих сити се земља.
14 Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
Дајеш те расте трава стоци, и зелен на корист човеку, да би извадио хлеб из земље.
15 ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
И вино весели срце човеку, и лице се светли од уља, и хлеб срце човеку крепи.
16 Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
Сите се дрвета Божија, кедри ливански, које си посадио.
17 A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
На њима птице вију гнезда; станак је родин на јелама.
18 Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
Горе високе дивокозама, камен је уточиште зечевима.
19 Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
Створио си месец да показује времена, сунце познаје запад свој.
20 Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
Стереш таму, и бива ноћ, по којој излази све зверје шумско;
21 Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
Лавови ричу за пленом, и траже од Бога хране себи.
22 Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
Сунце гране, и они се сакривају и лежу у ложе своје.
23 Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
Излази човек на посао свој, и на рад свој до вечера.
24 Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
Како је много дела Твојих, Господе! Све си премудро створио; пуна је земља блага Твог.
25 Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
Гле, море велико и широко, ту гмижу без броја, животиња мала и велика;
26 A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
Ту лађе плове, крокодил, ког си створио да се игра по њему.
27 Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
Све Тебе чека, да им дајеш пићу на време.
28 Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
Дајеш им, примају; отвориш руку своју, сите се добра.
29 Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
Одвратиш лице своје, жалосте се; узмеш им дух, гину, и у прах свој враћају се.
30 Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
Пошаљеш дух свој, постају, и понављаш лице земљи.
31 Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
Слава Господу увек; нек се весели Господ за дела своја!
32 shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
Он погледа на земљу, и она се тресе; дотакне се гора, и диме се.
33 Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
Певаћу Господу за живота свог; хвалићу Бога свог док сам год.
34 Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
Нека Му буде мила беседа моја! Веселићу се о Господу.
35 Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.
Нека нестане грешника са земље, и безбожника нека не буде више! Благосиљај, душо моја, Господа! Алилуја!

< Zabura 104 >