< Zabura 103 >

1 Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
[A Psalm] of David. Bless the Lord, O my soul; and all [that is] within me, [bless] his holy name.
2 Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Bless the Lord, O my soul, and forget not all his praises:
3 wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
who forgives all thy transgressions, who heals all thy diseases;
4 wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
who redeems thy life from corruption; who crowns thee with mercy and compassion;
5 Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
who satisfies thy desire with good things: [so that] thy youth shall be renewed like [that] of the eagle.
6 Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
The Lord executes mercy and judgment for all that are injured.
7 Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
He made known his ways to Moses, his will to the children of Israel.
8 Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
The Lord is compassionate and pitiful, long-suffering, and full of mercy.
9 Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
He will not be always angry; neither will he be wrathful for ever.
10 ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
He has not dealt with us according to our sins, nor recompensed us according to our iniquities.
11 Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
For as the heaven is high above the earth, the Lord has [so] increased his mercy toward them that fear him.
12 kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
As far as the east is from the west, [so far] has he removed our transgressions from us.
13 Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
As a father pities [his] children, the Lord pities them that fear him.
14 gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
For he knows our frame: remember that we are dust.
15 Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
[As for] man, his days are as grass; as a flower of the field, so shall he flourish.
16 iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
For the wind passes over it, and it shall not be; and it shall know its place no more.
17 Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
But the mercy of the Lord is from generation to generation upon them that fear him, and his righteousness to children's children;
18 tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
to them that keep his covenant, and remember his commandments to do them.
19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
The Lord has prepared his throne in the heaven; and his kingdom rules over all.
20 Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Bless the Lord, all ye his angels, mighty in strength, who perform his bidding, [ready] to hearken to the voice of his words.
21 Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Bless the Lord, all ye his hosts; [ye] ministers of his that do his will.
22 Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Bless the Lord, all his works, in every place of his dominion: bless the Lord, O my soul.

< Zabura 103 >