< Karin Magana 8 >

1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Doesn't wisdom cry out? Doesn't understanding raise her voice?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
On the top of high places by the way, where the paths meet, she stands.
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
Beside the gates, at the entry of the city, at the entry doors, she cries aloud:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
"To you men, I call. I send my voice to the sons of humankind.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
You simple, understand prudence. You fools, be of an understanding heart.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Hear, for I will speak excellent things. The opening of my lips is for right things.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
For my mouth speaks truth. Wickedness is an abomination to my lips.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
All the words of my mouth are in righteousness. There is nothing crooked or perverse in them.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
They are all plain to him who understands, right to those who find knowledge.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Receive my instruction rather than silver; knowledge rather than choice gold.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
For wisdom is better than rubies. All the things that may be desired can't be compared to it.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
"I, wisdom, have made prudence my dwelling. Find out knowledge and discretion.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
The fear of YHWH is to hate evil. I hate pride, arrogance, the evil way, and the perverse mouth.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Counsel and sound knowledge are mine. I have understanding and power.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
By me kings reign, and rulers decree justice.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
By me princes rule; nobles, and all the righteous rulers of the earth.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
I love those who love me. Those who seek me diligently will find me.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
With me are riches, honor, enduring wealth, and prosperity.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
My fruit is better than gold, yes, than fine gold; my yield than choice silver.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
I walk in the way of righteousness, in the midst of the paths of justice;
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
That I may give wealth to those who love me. I fill their treasuries.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
"YHWH created me in the beginning of his way, before his works of old.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
I was set up from everlasting, from the beginning, before the earth existed.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
When there were no depths, I was brought forth, when there were no springs abounding with water.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Before the mountains were settled in place, before the hills, I was brought forth;
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
while as yet he had not made the earth, nor the fields, nor the beginning of the dust of the world.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
When he established the heavens, I was there; when he set a circle on the surface of the deep,
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
when he established the clouds above, when the springs of the deep became strong,
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
when he gave to the sea its boundary, that the waters should not violate his commandment, when he marked out the foundations of the earth;
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
then I was the craftsman by his side. I was a delight day by day, always rejoicing before him,
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
Rejoicing in his whole world. My delight was with the sons of men.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
"Now therefore, son, listen to me, for blessed are those who keep my ways.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Hear instruction, and be wise. Do not refuse it.
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Blessed is the man who hears me, watching daily at my gates, waiting at my door posts.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
For whoever finds me, finds life, and will obtain favor from YHWH.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
But he who sins against me wrongs his own soul. All those who hate me love death."

< Karin Magana 8 >