< Karin Magana 25 >

1 Waɗannan ƙarin karin maganar Solomon ne waɗanda mutanen Hezekiya sarkin Yahuda suka tara.
These, too, are parables of Solomon, which the men of Hezekiah, king of Judah, transferred.
2 Ɗaukakar Allah ce a ɓoye batun; a bayyana batun kuwa ɗaukakar sarakuna ne.
It is to the glory of God to conceal a word, and it is to the glory of kings to investigate speech.
3 Kamar yadda sammai suna can bisa duniya kuma tana da zurfi, haka zukatan sarakuna suka wuce a bincika.
Heaven above, and earth below, and the heart of kings are each unsearchable.
4 Ka tace azurfa sai kayan su fito don maƙerin azurfa;
Take away the tarnish from silver, and a most pure vessel will go forth.
5 ka cire mugaye daga gaban sarki, kursiyinsa kuwa zai kahu ta wurin adalci.
Take away impiety from the face of the king, and his throne shall be made firm by justice.
6 Kada ka ɗaukaka kanka a gaban sarki, kada kuma ka nemi wa kanka wuri a cikin manyan mutane;
Do not appear glorious before the king, and do not stand in the place of the great.
7 gara ya ce maka, “Ka hauro nan,” da a ƙasƙantar da kai a gaban wani mai makami. Abin da ka gani da idanunka
For it is better that it should be said to you, “Ascend to here,” than that you should be humbled before the prince.
8 kada ka yi garaje kai ƙara a majalisa, gama me za ka yi a ƙarshe in maƙwabcinka ya ba ka kunya?
The things that your eyes have seen, do not offer hastily in a quarrel, lest afterward you may not be able to make amends, when you have dishonored your friend.
9 In kai da maƙwabcinka kuka yi gardama, kada ka tona asirin wani,
Argue your case with your friend, and do not reveal the secret to an outsider,
10 in ba haka ba duk wanda ya ji zai kunyata ka ba za ka kuma taɓa rabuwa da wannan mummuna suna ba.
lest perhaps he may insult you, when he has heard it, and he might not cease to reproach you. Grace and friendship free a man; preserve these for yourself, lest you fall under reproach.
11 Kalmar da aka faɗa daidai tana kamar zubin zinariyar da aka yi a mazubin azurfa.
Whoever speaks a word at an opportune time is like apples of gold on beds of silver.
12 Kamar’yan kunnen zinariya ko kuwa kayan ado na zinariya zalla haka yake da tsawatawar mai hikima ga kunne mai saurarawa.
Whoever reproves the wise and obedient ear is like an earring of gold with a shining pearl.
13 Kamar sanyin ƙanƙara a lokacin girbi haka ɗan saƙo mai aminci wanda aka aika; ya wartsakar da ran waɗanda suka aike shi.
Just like the cold of snow in a time of harvest, so also is a faithful messenger to him who sent him: he causes his soul to rest.
14 Kamar gizagizai da kuma iska marar ruwan sama haka mutumin da yake fariya a kan kyautan da ba ya bayarwa.
A man who boasts and does not fulfill his promises is like clouds and wind, when rain does not follow.
15 Ta wurin haƙuri akan rinjaye mai mulki, magana mai hankali kan karye ƙashi.
By patience, a leader shall be appeased, and a soft tongue shall break hardness.
16 In ka sami zuma, ka sha isashe kawai, in ya yi yawa, za ka yi amai.
You have discovered honey; eat what is sufficient for you, lest perhaps, being filled up, you may vomit it.
17 Kada ka cika ziyarar gidan maƙwabcinka yawan ganinka zai sa ya ƙi ka.
Withdraw your feet from the house of your neighbor, lest, when he has had his fill, he may hate you.
18 Kamar sanda ko takobi ko kibiya mai tsini haka yake da mutumin da yake ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinsa.
A man who speaks false testimony against his neighbor is like a dart and a sword and a sharp arrow.
19 Kamar haƙori mai ciwo ko yin tafiya da gurguwar ƙafa haka yake ga mai dogara da marasa aminci a lokacin wahala.
Whoever sets his hopes on the unfaithful in a day of anguish is like a rotten tooth and weary foot,
20 Kamar wanda ya tuɓe riga a ranar da ake sanyi, ko kuwa kamar zuba ruwan tsami a kanwa, haka yake da mai rera waƙoƙi ga mai baƙin ciki.
and like one who loosens his garment in cold weather. Whoever sings verses to a wicked heart is like vinegar on baking soda. Just like a moth to a garment, and a worm to wood, so too does the sadness of a man do harm to the heart.
21 In abokin gābanka yana jin yunwa, ka ba shi abinci ya ci; in yana jin ƙishi, ka ba shi ruwa ya sha.
If your enemy is hungry, feed him. If he is thirsty, give him water to drink.
22 Ta yin haka, za ka tara garwashin wuta mai ci a kansa, Ubangiji kuma zai sāka maka.
For you will gather hot coals upon his head, and the Lord will repay you.
23 Kamar yadda iskar arewa kan kawo ruwan sama, haka jita-jita kan kawo fushi.
The north wind brings forth the rain, and a sorrowful face brings forth a detracting tongue.
24 Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
It is better to sit in a corner of the attic, than with an argumentative woman and in a shared house.
25 Kamar ruwan sanyi ga ran da ya gaji haka yake da jin labari mai daɗi daga ƙasa mai nisa.
Like cold water to a thirsty soul, so too are good reports from a far away land.
26 Kamar rafi mai laka ko rijiyar da ta gurɓace haka yake da mai adalci wanda ya miƙa wuya ga mugaye.
The just falling down before the impious is like a fountain stirred up by feet and like a corrupted spring.
27 Ba shi da kyau ka sha zuma da yawa, haka ma ba shi da kyau ka nemi girma wa kanka.
Just as whoever eats too much honey, it is not good for him, so also whoever is an investigator of what is majestic will be overwhelmed by glory.
28 Kamar birni da katangarsa sun rushe haka yake da mutumin da ba ya iya danne fushinsa.
Just like a city lying in the open and without surrounding walls, so also is a man who is unable to restrain his own spirit in speaking.

< Karin Magana 25 >