< Karin Magana 24 >

1 Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
Não tenhas inveja dos homens malignos, nem desejes estar com eles,
2 gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
Porque o seu coração medita a rapina, e os seus lábios falam a malícia.
3 Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
Com a sabedoria se edifica a casa, e com a inteligência se estabelece:
4 ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
E pelo conhecimento se encherão as câmaras de todas as substâncias preciosas e deleitáveis.
5 Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
E o varão sábio é forte, e o varão de conhecimento consolida a força.
6 don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
Porque com conselhos prudentes tu farás a guerra; e há vitória na multidão dos conselheiros.
7 Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
É demasiadamente alta para o tolo toda a sabedoria; na porta não abrirá a sua boca.
8 Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
Aquele que cuida em fazer mal mestre de maus intentos o chamarão.
9 Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
O pensamento do tolo é pecado, e é abominável aos homens o escarnecedor.
10 In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
Se te mostrares frouxo no dia da angústia, a tua força será estreita.
11 Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
Livra aos que estão tomados para a morte, e aos que levam para matança, se os poderes retirar.
12 In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
Se disseres: Eis que o não sabemos: porventura aquele que pondera os corações não o entenderá? e aquele que atenta para a tua alma não o saberá? porque pagará ao homem conforme a sua obra.
13 Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
Come mel, meu filho, porque é bom, e o favo de mel é doce ao teu paladar.
14 Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Tal será o conhecimento da sabedoria para a tua alma: se a achares, haverá para ti galardão, e não será cortada a tua expectação.
15 Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
Não espies a habitação do justo, ó ímpio, nem assoles a sua câmara.
16 gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
Porque sete vezes cairá o justo, e se levantará; mas os ímpios tropeçarão no mal
17 Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
Quando cair o teu inimigo, não te alegres, nem quando tropeçar se regozije o teu coração.
18 in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
Para que o Senhor o não veja, e seja mau aos seus olhos, e desvie dele a sua ira.
19 Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
Não te indignes acerca dos malfeitores, nem tenhas inveja dos ímpios,
20 gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
Porque o maligno não terá galardão, e a lâmpada dos ímpios se apagará.
21 Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
Teme ao Senhor, filho meu, e ao rei, e não te entremetas com os que buscam mudança.
22 gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
Porque de repente se levantará a sua perdição, e a ruína deles ambos quem a sabe?
23 Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
Também estes são provérbios dos sábios: Ter respeito a pessoas no juízo não é bom.
24 Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
O que disser ao ímpio: Justo és: os povos o amaldiçoarão, as nações o detestarão.
25 Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
Mas para os que o repreenderem haverá delícias, e sobre eles virá a benção do bem
26 Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
Beijados serão os lábios do que responde com palavras retas.
27 Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
Prepara de fora a tua obra, e aparelha-a no campo, e então edifica a tua casa.
28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
Não sejas testemunha sem causa contra o teu próximo; porque enganarias com os teus beiços?
29 Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
Não digas: Como ele me fez a mim, assim o farei eu a ele: pagarei a cada um segundo a sua obra.
30 Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
Passei pelo campo do preguiçoso, e junto à vinha do homem falto de entendimento;
31 ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
E eis que toda estava cheia de cardos, e a sua superfície coberta de ortigas, e a sua parede de pedra estava derribada.
32 Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
O que tendo eu visto, o tomei no coração, e, vendo-o, recebi instrução.
33 Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
Um pouco de sono, adormecendo um pouco; encruzando as mãos outro pouco, para estar deitado.
34 sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.
Assim te sobrevirá a tua pobreza como um caminhante, e a tua necessidade como um homem armado.

< Karin Magana 24 >