< Karin Magana 20 >

1 Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
Il vino [è] schernitore, e la cervogia [è] tumultuante; E chiunque ne è vago non è savio.
2 Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
Il terrore del re [è] come il ruggito del leoncello; Chi lo provoca ad indegnazione pecca [contro a] sè stesso.
3 Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
[Egli è] gloria all'uomo di rimanersi di contesa; Ma chiunque è stolto si fa schernire.
4 Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
Il pigro non ara per cagion del freddo; [E poi] nella ricolta va accattando, e [non trova] nulla.
5 Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
Il consiglio nel cuor dell'uomo [è] un'acqua profonda; E l'uomo intendente l'attignerà.
6 Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
Il più degli uomini predicano ciascuno la sua benignità; Ma chi troverà un uomo verace?
7 Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
I figliuoli del giusto, che cammina nella sua integrità, [Saranno] beati dopo di lui.
8 Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
Il re, sedendo sopra il trono del giudicio, Dissipa ogni male con gli occhi suoi.
9 Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
Chi può dire: Io ho purgato il mio cuore, Io son netto del mio peccato?
10 Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
Doppio peso, e doppio staio, [Sono] amendue cosa abbominevole al Signore.
11 Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
Fin da fanciullo [l'uomo] è riconosciuto da' suoi atti, Se egli [sarà] puro, e se le sue opere [saranno] diritte.
12 Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
Il Signore ha fatte amendue queste cose: E l'orecchio che ode, e l'occhio che vede.
13 Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
Non amare il sonno, che tu non impoverisca; Tieni gli occhi aperti, [e] sarai saziato di pane.
14 “Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
Chi compera dice: [Egli è] cattivo, [egli è] cattivo; Ma quando se n'è andato, allora si vanta.
15 Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
Vi è dell'oro, e delle perle assai; Ma le labbra di scienza [sono] un vaso prezioso.
16 A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
Prendi pure il vestimento di chi ha fatta sicurtà per lo strano; Prendi pegno da lui per gli stranieri.
17 Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
Il pane acquistato con frode è soave all'uomo; Ma poi la sua bocca si trova piena di ghiaia.
18 Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
I disegni son renduti stabili con consiglio; Fa' dunque la guerra con prudenti deliberazioni.
19 Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
Chi va sparlando palesa il segreto: Non rimescolarti adunque con chi è allettante di labbra.
20 In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
La lampana di chi maledice suo padre, o sua madre, Sarà spenta nelle più oscure tenebre.
21 Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
L'eredità acquistata di subito da principio Non sarà benedetta alla fine.
22 Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
Non dire: Io renderò il male; Aspetta il Signore, ed egli ti salverà.
23 Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
Doppio peso [è] cosa abbominevole al Signore; E le bilance fallaci non [sono] buone.
24 Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
I passi dell'uomo [sono] dal Signore; E come intenderà l'uomo la sua via?
25 Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
Dire inconsideratamente: [Questa è] cosa sacra; E riflettere dopo aver fatti i voti, è un laccio all'uomo.
26 Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
Il re savio dissipa gli empi, E rimena la ruota sopra loro.
27 Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
L'anima dell'uomo [è] una lampana del Signore, Che investiga tutti i segreti nascondimenti del ventre.
28 Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
Benignità e verità guardano il re; Ed egli ferma il suo trono per benignità.
29 Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
La forza de' giovani [è] la lor gloria; E l'onor de' vecchi [è] la canutezza.
30 Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.
I lividori delle battiture, e le percosse che penetrano addentro nel ventre [Sono] una lisciatura nel malvagio.

< Karin Magana 20 >